Fasinjoji sun yi cirko-cirko a babban filin jirgin saman Kenya ranar Talata yayin da yajin aikin da masu kula da zirga-zirgar jiragen sama ya shiga rana na biyu, wanda ya bar wasu matafiya suna jira tsawon sa'o'i, wasu kuma ba su da tabbas ko jiragensu za su tashi kwata-kwata.
Yajin aikin ya haifar da babban cikas a filin jirgin saman Jomo Kenyatta na Nairobi, daya daga cikin cibiyoyin sufurin jiragen sama mafi cunkoso a Afirka.
Kamfanin jirgin saman kasa na Kenya Airways ya ce a ranar Talata yana ganin za a samu jinkirin tashi har zuwa awanni hudu.
Kamfanin jirgin saman Uganda Airlines ya ce an soke jiragensa guda biyu, yayin da Jambojet ya nemi fasinjoji da kada su yi tafi filin jirgin har sai an ba su umarni.
"An gaya mana mu jira har sai an sake sanarwa. Iyalina sun zo su gan ni, kuma har yanzu suna nan suna jirana," in ji fasinjan Kenya Jazzy Mwango yayin tattaunawa da Reuters.
Wata matafiya ‘yar kasar Kenya, Betty Wambui, ta ce sun yi niyyar tafiya zuwa Masar ta Qatar amma yanzu ta rude sosai domin ba ta san ko za ta yi tafiyar ba ko a'a.
Kungiyar Ma'aikatan Jiragen Sama ta Kenya ta fara yajin aikin a ranar Litinin, duk da umarnin kotu da ya ce bai kamata a yi ba.
Korafe-korafen da ƙungiyar ta yi wa Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Kenya sun haɗa da gazawar ta na cim ma yarjejeniyar ciniki ta gama gari da kuma sanya ma'aikata a kan wa'adin wucin gadi don ayyukan da ta ce na dindindin ne.
Hukumar kula da harkokin jiragen sama ta ce tana son warware takaddamar cikin lumana.
Ministan Sufuri ya kira ƙungiyar da hukumar kula da harkokin jiragen sama zuwa wani taro a ranar Talata don ƙoƙarin cim ma wa’adin.
Matafiya 'yan kasar Ghana Harry Frimpong da ɗan'uwansa Garry sun yi gaggawar zuwa filin jirgin sama bayan an gaya musu cewa jirginsu zai tashi. Amma da suka isa, sun ci gaba da kasancewa cikin rudani na tsawon sa'o'i da dama.
"Hakika yanayi ne mai ban takaici, amma na fahimci cewa dole ne ma'aikata su nemi haƙƙinsu," in ji Harry.












