| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An bar fasinjoji cirko-cirko a rana ta biyu ta yajin aikin ma'aikatan filin jirgin saman Kenya
Yajin aikin ma’aikatan filayen jiragen saman Kenya da ya shiga rana ta biyu ya kawo cikas ga jigilar fasinjoji a babban filin jiragen sama na Nairobi, inda aka soke da jinkirta tashin jirage, kuma an yi kira da a tattaunawa don magance matsalar.
An bar fasinjoji cirko-cirko a rana ta biyu ta yajin aikin ma'aikatan filin jirgin saman Kenya
Ma'aikata sun kawo cikas ga jirage a babban filin jirage na Kenya / Reuters / Reuters
17 Fabrairu 2026

Fasinjoji sun yi cirko-cirko a babban filin jirgin saman Kenya ranar Talata yayin da yajin aikin da masu kula da zirga-zirgar jiragen sama ya shiga rana na biyu, wanda ya bar wasu matafiya suna jira tsawon sa'o'i, wasu kuma ba su da tabbas ko jiragensu za su tashi kwata-kwata.

Yajin aikin ya haifar da babban cikas a filin jirgin saman Jomo Kenyatta na Nairobi, daya daga cikin cibiyoyin sufurin jiragen sama mafi cunkoso a Afirka.

Kamfanin jirgin saman kasa na Kenya Airways ya ce a ranar Talata yana ganin za a samu jinkirin tashi har zuwa awanni hudu.

Kamfanin jirgin saman Uganda Airlines ya ce an soke jiragensa guda biyu, yayin da Jambojet ya nemi fasinjoji da kada su yi tafi filin jirgin har sai an ba su umarni.

"An gaya mana mu jira har sai an sake sanarwa. Iyalina sun zo su gan ni, kuma har yanzu suna nan suna jirana," in ji fasinjan Kenya Jazzy Mwango yayin tattaunawa da Reuters.

Wata matafiya ‘yar kasar Kenya, Betty Wambui, ta ce sun yi niyyar tafiya zuwa Masar ta Qatar amma yanzu ta rude sosai domin ba ta san ko za ta yi tafiyar ba ko a'a.

Kungiyar Ma'aikatan Jiragen Sama ta Kenya ta fara yajin aikin a ranar Litinin, duk da umarnin kotu da ya ce bai kamata a yi ba.

Korafe-korafen da ƙungiyar ta yi wa Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Kenya sun haɗa da gazawar ta na cim ma yarjejeniyar ciniki ta gama gari da kuma sanya ma'aikata a kan wa'adin wucin gadi don ayyukan da ta ce na dindindin ne.

Hukumar kula da harkokin jiragen sama ta ce tana son warware takaddamar cikin lumana.

Ministan Sufuri ya kira ƙungiyar da hukumar kula da harkokin jiragen sama zuwa wani taro a ranar Talata don ƙoƙarin cim ma wa’adin.

Matafiya 'yan kasar Ghana Harry Frimpong da ɗan'uwansa Garry sun yi gaggawar zuwa filin jirgin sama bayan an gaya musu cewa jirginsu zai tashi. Amma da suka isa, sun ci gaba da kasancewa cikin rudani na tsawon sa'o'i da dama.

"Hakika yanayi ne mai ban takaici, amma na fahimci cewa dole ne ma'aikata su nemi haƙƙinsu," in ji Harry.

Rumbun Labarai
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin
Shugaban ƙasar Djibouti Guelleh ya sake yin nasara karo na shida
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Djibouti inda Guelleh da ke mulki ke neman wa'adi na shida
Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasa
Yadda ajujuwan Afirka ke fuskantar jarrabawa mafi tsauri a duniya
Kamaru ta ce ‘yan kasarta 16 sun mutu yayin taya Rasha yaki da Ukraine
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara
Ghana za ta fara aiwatar da shirin shiga ƙasar ba tare da biza ba ga dukkan 'yan Afirka
Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba
Sudan ta nemi 'yan ƙasar da suka yi ƙaura zuwa ƙasashen waje saboda yaƙi su koma gida
Hukumar leƙen asirin Somalia ta kashe masu haɗa bama-baman Al Shabab
Mali ta musanta rahoton sakin ’yanta’adda 200 domin samun man fetur
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Darasin da Togo ke koya wa sauran kasashe wajen magance cututtukan da aka yi watsi da su
’Yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 kusa da iyakar Nijar da Mali