AFIRKA
2 minti karatu
Burkina Faso ta ƙi karɓar mutanen da aka kora daga Amurka
Matakin na Burkina Faso ya zo ne a daidai lokacin da ofishin jakadancin Amurka da ke Ouagadougou babban birnin ƙasar ya dakatar da ayyukan biza, matakin da gwamnatin Traore ta kira ''bita-da-ƙulli''.
Burkina Faso ta ƙi karɓar mutanen da aka kora daga Amurka
Shugaban kasar Burkina Faso Ibrahim Taore
10 Oktoba 2025

Burkina Faso ta ki ƙarɓar mutanen da aka kora daga Amurka, a wani mataki na watsi da ɗaya daga cikin manufofin Shugaba Donald Trump kan baƙin-haure.

Tun bayan komawar Trump Fadar White House, gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen tura mutane zuwa ƙasashe marasa karfi, musamman ƙasashen da ba su da alaka da su, a wani ɓangare na ƙoƙarin yaki da baƙin-haure.

A cikin ‘yan kwanakin nan a Afirka, ƙasar Eswatini da Ghana da Rwanda da kuma Sudan ta Kudu duk sun amince da mutanen da aka kora daga Amurka.

Sai dai kuma da yammacin ranar Alhamis, Ministan Harkokin Wajen Burkina Faso ya bayyana cewa, ƙasarsa da ke yankin yammacin Afirka ta yi watsi da matakin da Washington ta ɗauka.

"Bisa ƙa'ida, wannan shawara da muka ɗauka ba ta dace ba a wancan lokacin, sannan ta saɓawa ƙa'idar mutunci na ɗan’adam," kamar yadda Karamoko Jean-Marie Traore ya bayyana ta gidan talabijin din.

Masu AlakaTRT Afrika - Ghana za ta karɓi ƙarin mutum 40 da za a kora daga Amurka

Martanin Amurka

Kafin matakin na Burkina Faso, ofishin jakadancin Amurka da ke Ouagadougou babban birnin ƙasar, ya sanar da dakatar da ayyukansa na ba da biza ga galibin mutanen da ke zaune a Burkina Faso.

A maimakon haka, a yanzu 'yan ƙasar za su samu biyan buƙata ne a Lome, babban birnin makwabciyar ƙasar Togo.

"Shin wannan wata hanya ce ta matsin lamba a garemu? Ko kuma bita-da-ƙulli ne? To ko ma mene ne ... Burkina Faso ƙasa ce mai daraja, kuma wurin zuwa, ba wurin koro mutane ba ne," in ji Karamoko Jean-Marie Traore.

Tun bayan karɓar mulki a shekarar 2022 shugaban ƙasar Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore, ya ɗaura ɗamarar ƙarfafa kyamar mulkin mallaka, tare da yin watsi da tsohuwar uwargijiyar ƙasar da ta yi mata mulkin mallaka wato Faransa da sauran kasashen yammacin duniya.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya