| hausa
DUNIYA
1 minti karatu
Kotun Bangladesh ta yanke wa Sheikh Hasina hukuncin kisa
“Duk wasu shika-shikan aikata laifuka kan bil’adama sun cika,” in ji alkalin kotun, Golam Mortuza Mozumder, yayin da yake karanta hukuncin ga kotun da ta cika maƙil a Dhaka.
Kotun Bangladesh ta yanke wa Sheikh Hasina hukuncin kisa
Hasina ta saba wa umarnin kotu na dawowa daga Indiya, inda ta gudu a bara.
17 Nuwamba 2025

Wata kotu a Bangladesh a ranar Litinin ta yanke wa tsohuwar Firaminista Sheikh Hasina hukuncin kisa kan laifukan cin zarafin bil’adama, inda aka yi ta murna a cikin kotun da a yayin da alƙali ke karanto hukuncin.

An bayyana cewa Hasina, mai shekaru 78, ta ƙi bin umarnin kotu da ke buƙatar ta dawo daga Indiya domin ta halarci shari’arta kan zargin cewa ta umarci amfani da ƙarfi wurin daƙile zanga-zangar ɗalibai wadda ta kai ga kifar da gwamnatin ta.

Wannan hukunci da jama’a suka dade suna jira, wanda aka watsa kai tsaye a talabijin na ƙasa, ya zo ne kafin zaɓen farko tun bayan kifar da ita a watan Agustan 2024.

 “Duk wasu shika-shikan aikata laifuka kan bil’adama sun cika,” in ji alkalin kotun, Golam Mortuza Mozumder, yayin da yake karanta hukuncin ga kotun da ta cika makil a Dhaka.

An bayyana cewa an same ta “da laifi a tuhuma uku,” ciki har da hura wutar tashin hankali, bayar da umarnin kashe mutane, da kuma rashin ɗaukar mataki don hana aikata munanan abubuwan da aka aikata, in ji Mozumder

“Mun yanke shawarar yanke mata hukunci guda ɗaya — wato hukuncin kisa.”

 

Rumbun Labarai
Hukumar Falasɗinawa ta yi maraba da shirin Kwamitin Tsaro na MDD kan Gaza
Koriya ta Kudu ta nemi yin tattaunawar soji da Koriya ta Arewa don kaucewa rikicin kan iyaka
Trump ya sayi takardun lamuni na aƙalla dala miliyan 82 tun daga Agustan 2025 – Bayanai
Trump ya bayar da umarnin haramta wa masu ƙiba shiga Amurka
Fadan 'yan daba da gwamnati ya jawo asarar rayuka 1,200 a cikin wata uku a Haiti - MDD
Numfashi na mana wahala saboda gurbacewar iska a birnin New Delhi na India
An soke tashin jiragen sama fiye da 2,000 a Amurka yayin da harkokin gwamnati ke ci gaba da dagulewa
Zinarin da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ke shigarwa ƙasarta daga Sudan ya ƙaru yayin da ake yaƙi
COP30: Manyan masu gurbata muhalli na duniya ba su je taron sauyin yanayi na Brazil ba
Rasha ta ce tana sa ido kan Nijeriya bayan barazanar da Trump ya yi ta kai hari kasar
Zohran Mamdani: Matashi Musulmi na farko ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York
Yadda amfani da magungunan antibiotic barkatai ya sa cututtuka suka zama makamai
Rundunar Sojin Ruwan Pakistan ta kama mugwayen ƙwayoyi na dala biliyan ɗaya a Tekun Arebiya
An gano sauro a karon farko a ƙasar Iceland
Yadda hukumomi a India suke farautar Musulmai da suke cewa 'Ina son Annabi Muhammad'
Putin ya gargaɗi Trump cewa bai wa Ukraine makamai mai linzamin Tomahawk zai jawo matsala tsakaninsu
Abin da muka sani game da mummunar arangamar kan iyaka tsakanin sojin Pakistan da Afganistan
Waiwayen 1903: An taɓa yi wa Yahudawa tayin Afirka, kamar yadda ake so a mayar da Falasɗinawa yanzu
An naɗa Sarah Mullally mace ta farko Shugabar Cocin Ingila
Yadda mutuwar ɓauna a turmutsutsu ke sauya salon farautar manyan namun dawa