Fiye da watanni shida bayan yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta shiga tsakani don dakatar da yaƙi, Gaza ta kasance wata ƙatuwar maƙabarta da ba a san iyakarta ba.
A cewar Hukumar Kare Fararen Hula ta Gaza da kuma wani rahoto na kwanan nan na jaridar Haaretz, aƙalla Falasdinawa 8,000 ne suka rage a maƙale a ƙarƙashin baraguzan gidajensu.
Duk da yarjejeniyar tsagaita wutar, sake gina yankin bai kankama ba, inda ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na tan miliyan 68 na baraguzan aka kwashe zuwa yanzu.
Girman barnar da aka yi yana da wuyar siffantawa.
Wani binciken haɗin gwiwa da Majalisar Ɗinkin Duniya, Bankin Duniya, da Tarayyar Turai suka gudanar ya ƙiyasta cewa kwashe ɓaraguzan kawai zai ci kuɗi sama da dala biliyan 1.7.
Alexander De Croo, Shugaban Shirin Ci Gaban Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP), ya tabbatar da cewa idan aka ci gaba da tafiya a hakan, za a ɗauki aƙalla shekaru bakwai kafin a kwashe duka ɓaraguzan yankin.
Wannan ƙalubale na sufuri ya ƙara riƙidewa sakamakon kasancewar nakiyoyin da ba su tashi ba da kuma gawarwakin dubban mutane da ke ruɓewa a wurin.
‘Takardu da Tsayawar Aiki’
Ga iyalai da dama a Gaza, jiran ba wai kawai jinkiri ba ne na tsarin gwamnati.
Ƙungiyoyin kare farar hula sun ci gaba da karɓar dubunnan kiran waya daga dangi waɗanda suka san ainihin wurin da gawarwakin masoyansu suke.
Sai dai kuma, ƙarancin manyan injuna da kayan aiki na musamman ya sa an dakatar da aikin tuno gawarwaki a wasu yankunan da aka fi yi wa barna, ciki har da unguwannin Shujaiyeh da Tuffah na birnin Gaza.
A yawancin lokuta, gawarwakin suna can ne bayan layin da ake kira (Yellow Line) — yankunan da har yanzu kai-tsaye suke ƙarƙashin ikon sojojin Isra’ila.
Ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa kamar Red Cross da Majalisar Ɗinkin Duniya sun gaya wa iyalai cewa dole ne a sami amincewar ɓangaren Isra’ila kafin a kwashe gawarwakin, tsarin da yawancin lokaci yake karewa ba tare da nasara ba.
Yarjejeniyar tsagaita wuta tana cikin barazana
Jinkirin farfaɗo da yankin yana zuwa ne yayin da keta yarjejeniyar tsagaita wuta ta watan Oktoban 2025 da Isra’ila ke yi kullum ta dagula lamarin.
Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta ba da rahoton cewa Isra’ila ta kashe Falasdinawa 828 tun bayan fara tsagaita wuta, wanda hakan ya ƙara yawan mutanen da aka kashe zuwa sama da 72,000 daga kisan ƙiyashin da aka shafe shekaru biyu ana yi.
Wannan ci gaba da kai hare-hare da Isra’ila ke yi ya tsorata ma’aikatan ceto da ’yankwangilar ƙasa da ƙasa daga hci gaba da ayyukansu, yayin da wuraren kare farar hula da motocin ɗaukar marasa lafiya ke ci gaba da kasancewa cikin hatsarin hare-hare.
Ko a wuraren da za a iya gudanar da aikin ma, lamarin yana cike ce-ce-ku-ce.
A Rafah, iyalai a yankin sun yi zanga-zanga kwanan nan kan wasu kamfanonin kwangila, inda suke zargin su da yin haɗin gwiwa da hukumomin Isra’ila don kwashe wuraren domin gina gidaje ba tare da izinin dangi da aka yi wa rasuwa ba.
Ga mutane da dama, kula da waɗannan gawarwaki ba aiki ne kawai na sufuri ba, a’a, lamari ne na haƙƙin ɗan’adam.
Kamar yadda wani mazaunin wurin ya bayyana: “Mutane suna da haƙƙin a san sunayensu, a binne su, kuma a yi musu makoki.”
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Buɗaɗɗiyar maƙabartar Gaza: Gawawwaki 8,000 sun maƙale, yayin da aikin kwashe ɓaraguzai ya tsaya cak
Sama da Falasdinawa 8,000 ne har yanzu ba a gani ba a ƙarƙashin tan miliyan 68 na baraguzai, yayin da ƙoƙarin fito da su ke fuskantar ƙarancin kayan aiki da kuma fargabar sabbin hare-hare.

Rumbun Labarai











