| Hausa
WASANNI
2 minti karatu
An nada Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar kwallon kafa ta Faransa
Zidane, mai shekara 54 tsohon ɗanwasan Faransa, zai soma aiki gadan-gadan a watan Satumba, inda zai jagoranci wasan da ƙasarsa za ta yi da Turkiyya a Gasar Lig ta UEFA Nations League ranar 25 ga Satumba.
An nada Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar kwallon kafa ta Faransa
Rabon Zidane da aikin koci tun shekarar 2021 lokacin da ya bar Real Madrid.

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Faransa ranar Talata ta naɗa Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar ƙwallon ƙafar ƙasar, inda ya maye gurbin Didier Deschamps wanda ya kwashe shekaru 14 a kan muƙamin.

Shugaban hukumar Philippe Diallo ya ce an naɗa Zidane a kan muƙamin ne bayan an tuntuɓi babban kwamitin ƙwallon ƙafa kuma ya sanya hannu a kan kwantaragin shekaru huɗu daga ranar 1 ga watan Agusta mai zuwa.

Zidane, mai shekara 54 tsohon ɗanwasan Faransa, zai soma aiki gadan-gadan a watan Satumba, inda zai jagoranci wasan da ƙasarsa za ta yi da Turkiyya a Gasar Lig ta UEFA Nations League ranar 25 ga Satumba.


Da yake jawabi bayan naɗin nasa, Zidane ya ce ya kwashe shekaru biyar yana ƙin karɓar tayin yin aikin koci saboda babu abin da yake so tamkar zama "kocin Faransa."


Zidane ya maye gurbin Deschamps, wanda ya zama kocin Faransa a 2012, inda ya kai ƙasar ga lashe Kofin Duniya na 2018 FIFA World Cup, da kuma zagayen ƙarshe na Gasar Kofin Duniya ta 2022, da zagayen kusa da ƙarshe na Gasar Kofin Duniya ta 2026 da kuma wasan ƙarshe na UEFA Euro 2016.

Rabon Zidane da aikin koci tun shekarar 2021 lokacin da ya bar Real Madrid.