| Hausa
WASANNI
2 minti karatu
An nada Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar kwallon kafa ta Faransa
Zidane, mai shekara 54 tsohon ɗanwasan Faransa, zai soma aiki gadan-gadan a watan Satumba, inda zai jagoranci wasan da ƙasarsa za ta yi da Turkiyya a Gasar Lig ta UEFA Nations League ranar 25 ga Satumba.
An nada Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar kwallon kafa ta Faransa
Rabon Zidane da aikin koci tun shekarar 2021 lokacin da ya bar Real Madrid.

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Faransa ranar Talata ta naɗa Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar ƙwallon ƙafar ƙasar, inda ya maye gurbin Didier Deschamps wanda ya kwashe shekaru 14 a kan muƙamin.

Shugaban hukumar Philippe Diallo ya ce an naɗa Zidane a kan muƙamin ne bayan an tuntuɓi babban kwamitin ƙwallon ƙafa kuma ya sanya hannu a kan kwantaragin shekaru huɗu daga ranar 1 ga watan Agusta mai zuwa.

Zidane, mai shekara 54 tsohon ɗanwasan Faransa, zai soma aiki gadan-gadan a watan Satumba, inda zai jagoranci wasan da ƙasarsa za ta yi da Turkiyya a Gasar Lig ta UEFA Nations League ranar 25 ga Satumba.


Da yake jawabi bayan naɗin nasa, Zidane ya ce ya kwashe shekaru biyar yana ƙin karɓar tayin yin aikin koci saboda babu abin da yake so tamkar zama "kocin Faransa."


Zidane ya maye gurbin Deschamps, wanda ya zama kocin Faransa a 2012, inda ya kai ƙasar ga lashe Kofin Duniya na 2018 FIFA World Cup, da kuma zagayen ƙarshe na Gasar Kofin Duniya ta 2022, da zagayen kusa da ƙarshe na Gasar Kofin Duniya ta 2026 da kuma wasan ƙarshe na UEFA Euro 2016.

Rabon Zidane da aikin koci tun shekarar 2021 lokacin da ya bar Real Madrid.

Rumbun Labarai
Masu ruwa da tsaki a ƙwallon ƙafar Nijeriya na taron tattauna hanyoyin kawo gyara
Falconets ta Nijeriya ta lallasa New Caledonia da ci 10-1, ta kai zagayen gaba a gasar Kofin Duniya
'A Maroko za a yi wasan ƙarshe na Kofin Duniya na 2030', in ji shugaban hukumar ƙwallon kasar
'An yi wa Arsenal fasha a wasansu da Aston Villa', in ji hukumar gasar Firimiya
NFF ta naɗa Eguavoen a matsayin kocin wucin-gadi na Super Falcons
An manta da Raphinha da Pedri cikin 'yanwasa 30 da za su iya lashe kyautar Ballon d'Or
Barcelona ta miƙa ƙoƙon-bara wajen masu zuba jari don neman kuɗin gyaran filin wasa
Turkiyya ta kuma lashe kofin gasar volleyball ta mata ta nahiyar Turai
An yanke wa Tiger Woods hukuncin haramcin tukin mota tsawon shekaru 5 saboda tuki cikin maye
Muhimman batutuwa game da ritayar Messi daga tawagar Argentina
Sakon Lionel Messi na yin ritaya daga buga kwallo a matakin kasa-da-kasa
"Jikina ya fara sakwarkwacewa" in ji Djokovic, bayan an fitar da shi daga Gasar US Open ta bana
Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya Musa Gusau ya yi murabus
Ɗanwasan Kamaru Carlos Baleba ya koma Man Utd daga Brighton
Habasha ta shiga takarar ɗaukar nauyin gasar AFCON ta 2028
An sayar da ƙwallon da Maradona ya ci Ingila da hannu a kan $3.35M
Ɗan Nijeriya Semi Ajayi ya taimaka wajen yi wa Man Utd dukan wulaƙanci a farkon Gasar Firimiya
Cristiano Ronaldo ya fara kakarsa ta 25 da ƙwallonsa na 977 a tarihin wasansa
EFCC ta fara binciken Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya, NFF
Jamal Musiala na Bayern Munich ya ce farfaɗiyar sandarewa ce ke damun sa