| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Shugaban Afirka ta Kudu Ramaphosa zai ƙalubalanci rahoton kwamiti kan rashin ɗa'a
Shugaba Cyril Ramaphosa ya ce zai nemi ƙarin haske na shari'a kan rahoton domin duba yiwuwar "babban kuskure na shari'a, da kuma cim ma wata matsaya mara tushe bisa gaskiya".
Shugaban Afirka ta Kudu Ramaphosa zai ƙalubalanci rahoton kwamiti kan rashin ɗa'a
Wani mutum yana kallo a talabijin yayin da Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa yake bayani ga ƙasar / Reuters

Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya bayyana ranar Litinin cewa shi ba zai yi murabus ba kuma ya ce zai shigar da ƙara domin ƙalubalantar shirin tsige shi game da badaƙalar zargin satar dala miliyan huɗu.

“Yayin da muka ga wasu kiraye-kiraye na neman na ajiye aiki, babau wani abu a cikin hukuncin kotun tsarin mulki da ya tilasta mini na ajiye muƙami na,” kamar yadda Ramaphosa ya bayyana a wani jawabin da ya yi a talabijin ga ‘yan ƙasar.

Lamarin ya sake fitowa ne a makon da ya gabata bayan kotun ta juya hukuncin watsi da wani rahoton majalisar dokoki na shekarar 2022 da ya ce Ramaphosa "ta yiwu ya aikata" babban ƙeta doka da rashin ɗa’a.

An zargi Shugaban ƙasar mai shekara 73 da laifin ɓoyewa daga ‘yansanda da hukumomin haraji wani kutse da satan kuɗaɗen ƙetare na shekarar 2020 da aka yi zargin cewa an ɓoye a cikin kujeru da gadaje a gidan gonarsa na alfarma a lardin arewaci na Limpopo.

A wani jawabi da ya yi bisa talabijin , Ramaphosa ya ce babu wani abu a hukuncin ranar Juma’a na kotun tsarin mulki da ya isa hujja ga tsige shi ko kuma cire shi daga muƙaminsa.

Rahoton Majalisar dokoki “na da rauni”

"Sabida haka bisa girmamawa ina so na bayyana cewa ba za ni ajiye aiki na ba," in ji shi , yana mai ƙarawa da cewa idan ya yi hakan, zai "ba da gaskatawa" ga rahoton majalisar dokoki "mai rauni" ne.

"Ina nan ba za ni ajiye aiki ba," in ji shi.

Wani kwamiti mai zaman kansa ya ce Ramaphosa "zai yiwu ya aikata " wasu jerin ƙeta doka masu muni da rashin ɗa’a dagane da kutsen.

Amma majalisar dokoki ,wadda a wancan lokacin jam’iyyarsa ta ANC ce ke jagorantarta, ta ƙi a shekarar 2022 ta buɗe shirin tsige da zai iya tilasta masa barin mulkin ƙasar.

Kotun tsarin mulkin ya ba da umarnin cewa a tura rahoton kwamitin zuwa wani kwamiti na tsige shi, a matsayin wani martani ga ƙorafin da jam’iyyar EFF mai rajin neman daidaito na tattalin arziki ya shigar.

Zaɓuka masu zuwa

Jam’iyyar ANC tana rasa goyon baya game da alƙawurran manufofi da ba ta cika ba da kuma zarge-zargen da ake ta yi mata na cin hanci da rashawa da raunin mulki, gabannin zaɓukan ƙananan hukumomi da za a yi ranar 4 ga watan Nuwamba.

Ramaphosa, wanda ofishinsa ya bayyana a makon da ya gabata cewa ta "lura" kuma ta girmama hukuncin kotun, ya bayyana a jawabinsa cewa an ba shi shawarar neman ƙarin haske na shari’a game da rahoton kwamitin.

Zai yi nazari game da yiwuwar "kuskure kan aikata muhimman kura-kurai, da kuma cim ma matsaya da ba ta da tushe bisa gaskiya", in ji shi.

Ramaphosa, wani tsohon mai gwagwarmayar yaƙi da mulkin wariyar launin fata wanda ya zama ɗankasuwa kafin ya shiga siyasa, ya musanta aikata ba daidai ba a badaƙalar.

Ya ce lallai an yi kusten, amma ya musanta iƙirarin wani toshon shugaban hukumar leƙen aisri cewa shi ya sa a saci ɓarayin a wani ƙoƙari na rufa-rufa kan batun.

Ya ce shi ya ba da rahoto game da kutsen ga ‘yansanda kuma ya bayyana cewa kuɗin ya samu ne daga sayar da ɓauna 20 kan kuɗi $580,000.

Rumbun Labarai
Nijar ta dakatar da kafafen yada labarai na Faransa guda 10
Kenya ta zaɓi amfani da 'fetur mai datti' saboda yaƙin Iran da ya kawo cikas ga jigilar mai
Masu haƙar zinari ba bisa ƙa'ida ba biyar sun maƙale a ƙarƙashin ƙasa bayan rami ya rufta a Zambia
Chadi ta ayyana zaman makoki na ƙasa bayan Boko Haram ta kashe sojojinta
Burkina Faso ta sake haramta wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda adadin ya kai 205
Rundunar sojin Chadi ta ce an kashe jami'anta 23 a wani harin Boko Haram
Afirka ta Kudu na bincike kan satar makaman soji
Harin jirgi mara matuƙi a Sudan ya kashe ’yan’uwa tara na wani kwamandan da ke mara wa soji baya
Mali tana binciken sojoji da ’yan siyasa da ke da alaƙa da hare-haren ta’addanci
’Yan tawaye sun ƙwace muhimmin sansani daga sojojin Mali da sojojin haya na Rasha - rahotanni
Amurka ta amince a sayar wa Isra’ila, UAE, Kuwait, Qatar makaman da suka haura na dala biliyan 8.6
Masana kimiyya a Kenya suna bincike don habaka yi wa kwayoyin halittar shanu kwaskwarima
Harin ta'addanci a Burkina Faso ya yi ajalin mutane 11
Mali za ta yi faretin soji na ban girma a jana'izar ministan tsaron da aka kashe a harin ta'addanci
Chadi ta kama tare da korar 'yan Nijeriya da suka guje wa 'yanta'adda
Ghana na neman ‘yankasuwa masu zuba jari a sabon kamfanin jiragen saman Ƙasar
Shugaban Mali ya ce komai ya 'koma daidai' a jawabinsa na farko tun bayan hare-haren 'yanta'adda
Ghana ta ƙi karɓar tallafin lafiya na Amurka na dala miliyan 109 bisa damuwa kan tsaron bayanai
An kashe mutum 10 tare da kama 11 a harin 'yanbindiga kan ayarin sojin Ghana
Ministan Tsaron Mali Camara ya yi musayar wuta da 'yanta'adda kafin a kashe shi