Wani tsohon jami’in sojojin Nijeriya mai ritaya, Manjo Janar Abubakar Rabe, tare da matarsa, waɗanda aka yi garkuwa da su mako guda da ya wuce a kan hanyar Karaduwa–Matazu a Jihar Katsina, sun roƙi gwamnati da ta gaggauta yin duk abin da ya dace domin ceto rayuwarsu.
Masu garkuwar sun fitar da wani bidiyo da ke nuna ma’auratan a cikin daji a tsare. A cikin bidiyon mai tsawon mintuna huɗu da daƙiƙa biyu da ke yawo a kafafen sada zumunta, an gansu a tsaye suna karanta buƙatun da masu garkuwar suka umurce su.
A cikin bidiyon, matar tsohon janar ɗin ta bayyana cewa masu garkuwar na neman a saki mambobinsu uku waɗanda suka haɗa da Sani, Aminu, da Nasiru. Haka kuma suna neman a mayar musu da dabbobin da ake zargin an ƙwace daga hannunsu.
Ta bayyana cewa an kama biyu daga cikin waɗanda ake tsare da su a Jikamshi, yayin da aka kama na uku a Kano.
Ta ƙara da roƙon gwamnatin Jihar Katsina da shugabannin ƙananan hukumomi biyar da su shiga tsakani domin a biya waɗannan buƙatu domin samun ’yancinsu.
Shi ma tsohon janar ɗin ya yi gajeriyar magana a cikin bidiyon, inda ya yi kira da a kwantar da hankali tare da neman a yi ƙoƙarin samar da zaman lafiya, yana mai cewa masu garkuwar sun nuna sha’awar tattaunawa da zaman lafiya.
Ba a ambaci neman kuɗin fansa a cikin bidiyon ba.
Rahotanni sun ce Manjo Janar ɗin mai ritaya yana kan hanyar tafiya zuwa Katsina a ranar Asabar tare da matarsa, Hajiya Amina Abubakar, da direbansu, Abdullahi Sa’idu, lokacin da aka tare motocinsu a kan hanyar Marabar Musawa–Kafinsoli a ƙaramar hukumar Matazu.












