TURKIYYA
2 minti karatu
Shekaru biyu na kisan kiyashi a Gaza: Emine Erdogan ta buƙaci a haɗa kai don yaƙar zalunci
A cikin shekaru biyu da suka wuce, Gaza ta zama maƙabarta inda aka kashe fiye da mutane 67,000 da ba su ji ba ba su gani ba, ciki har da yara fiye da 20,000, a cewar matar shugaban Turkiyya Emine Erdogan.
Shekaru biyu na kisan kiyashi a Gaza: Emine Erdogan ta buƙaci a haɗa kai don yaƙar zalunci
Erdogan ta ce a cikin shekaru biyu da suka gabata, Gaza ta koma makabarta.
8 Oktoba 2025

Matar shugaban ƙasar Turkiyya Emine Erdogan ta yi jimamin cika shekaru biyu na yaƙin Isra'ila a Gaza, inda ta yi tir da abin da ta bayyana a matsayin yunƙurin Isra'ila na shafe al'ummar Falasɗinu daga doron duniya.

"Ƙasar da ta rasa mutuncinta tana ƙoƙarin ruguza al'ummar Falasɗinu daga doron duniya,’’ a cewar wani saƙo da Erdogan ta wallafa a shafinta na NSosyal na Turkiyya.

"Duk da cewa zaluncin azzaluman na ƙaruwa, ƙarfin muryoyin haɗin-kai na tasirin kan kisan ƙare-dangi," in ji ta.

Erdogan ta ce, a cikin shekaru biyu da suka wuce, Gaza ta zama maƙabarta inda aka kashe mutane fiye da 67,000 da ba su ji ba ba su gani ba, ciki har da yara fiye da 20,000.

Ta jadadda cewa, a hare-hare da Isra’ila ke kaiwa, ‘‘babu wani mutunci, ko doka ko jinƙai, ko kuma ɗa’a da ba a keta shi ba."

Emine Erdogan ta ƙara da cewa, masu aikin sa-kai suna yin gangami don Gaza daga kowane lungu da saƙo na duniya, ta sama, ta ƙasa, da kuma ta ruwa, tana nuni ne kan ayarin jiragen ruwa na Sumud na baya bayan nan da suka yi ƙoƙarin zuwa yankin da aka yi wa ƙawanya, ta kuma yi kira ga “duk wani mutum mai tausayi da ya shiga wannan fafutuka da kuma haɗa kai a matsayin ɗaya daga cikin Falasɗinawa har sai an samu zaman lafiya mai ɗorewa.”

"Ina tunawa da 'yan’uwanmu Falasɗinawa da suka yi shahada a hare-haren Isra'ila, kuma ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki da ya sassauta wa al'ummar Falasɗinu tare da ƙara masu haƙuri da juriya da tsayin daka. #EndlessGenocideGaza," in ji ta.

Saƙon ya kuma haɗa da wani bidiyo da ke ɗauke da jawaban Emine Erdogan na baya kan Gaza da kuma hotuna da ke nuna ɓarnar da aka yi a yankin.

Rumbun Labarai
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro
Turkiyya ta yi maraba da amincewar majalisar dokokin TRCN kan ƙudurin samar da ƙasashe biyu
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan
Jami'an Turkiyya da Syria sun gudanar da tattaunawa kan tsaro a Ankara