| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Mutum 33 sun mutu, 33 sun jikkata a wata uku sakamakon hatsarin wutar lantarki a Nijeriya
Rahoton Q3 na 2025 ya bayyana cewa jimilla hatsarin da ke da alaka da lantarki 57 ne ya afku a fadin kasar a wannan lokaci.
Mutum 33 sun mutu, 33 sun jikkata a wata uku sakamakon hatsarin wutar lantarki a Nijeriya
Mahukuntan NERC na daukar matakan kariya da hana afkuwar hadurran a nan gaba. / Reuters
13 Janairu 2026

Alkaluman baya bayan nan game da lantarki da Hukumar Kula da Lantarki ta Nijeriya ta fitar sun bayyana mutuwar mutum 33, yayin da wasu 33 kuma suka jikkata sakamakon hatsarin da ke da alaa da lantarki a fadin kasar.

Rahoton Q3 na 2025 ya bayyana cewa jimillar hatsarin da ke da alaka da lantarki 57 ne ya afku a fadin kasar a wannan lokaci.

An samu hatsari a wurare daban-daban, inda cibiyoyin lantarki na Ikeja da Kano ke da mafi yawan hatsarin a watanni uku na ukun 2025.

Dukkan yankunan biyu sun fuskanci hatsari sau 10. Sannan Ikeja ta fuskanci rasa rayuka hudu da jikkatar mutum shida, sai Kano da ta samu asarar rayuka 6 da jikkatar mutum hudu.

A yayin da Abuja, Jos, Aba, Port Harcourt, Enugu da Yola suka fuskanci hatsari daban-daban, Eko, Kaduna da TCN ma sun shiga jerin. Aan samu raunuka sosai daga cikin hadarurrukan.

An bayyana cewa rashin bin ka’idar aiki da mummunan yanayi ne suka janyo mafi yawan hadurran da ma yawaitar jikkata, inda tsinkewa da fitar waya suka janyo mutuwar mutane 10 da jikkatar wasu 7.

An alakanta mutuwa 10 da jikkata 18 ga sakacin aikin da rashin bin ka’ida, inda aka samu kuskuren ma’aikata, rashin daukar matakan kariya da suka kamata da rashin ma’aikatan da ke da lasisin yin aikin.

Shiga wuraren da kayan wuta suke ba tare da izini ko ta barauniyar hanya ma sun janyo afkuwar hadurran, inda aka samu jikkatar mutane uku a wannan lokaci.

Barna ba ta janyo hatsari da yawa ba, amma kuma ta janyo mutuwar mutane biyu.

A nata bangaren, Hukumar ta NERC ta ce ta fara gudanar da bincike kan dukkan hatsarin d aaka rawaito ya afku da ma kayan da suka fashe, kamawar gobara da ayyukan barna a watanni ukun.

Hukumar gudanarwar ta kuma kara da cewa ta shirya taron masu ruwa da tsaki da ke da manufar inganta hanyoyin kariya a cibiyoyin, inda aka tattara jami’an lafiya da bayar da kariya daga kamfanonin lantarki don duba hadurran da suka afku, su bayyana kwarewarsu da darussan da aka dauka, sannan su samar da hanyoyin inganta yanayin da ake ciki.

A rahoton Q2 da aka fitar an bayyana samun hatsari 60 a cibiyoyin lantarki, an samu jikkatar mutane 19.

Rumbun Labarai
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya