13 awanni baya
An kashe sojoji takwas ranar Laraba a wani hari da wata ƙungiyar ta’addanci mai alaƙa da Daesh- ISWAP- ta kai a arewa maso gabashin Nijeriya, kamar yadda kafofin watsa labaran ƙasar suka ruwaito.
Wani jami’in soji ya ce mayaƙan ISWAP sun kai hari kan wani sansanin soji a ƙauyen Kauwa na jihar Borno.
Jami’in ya ce sojoji 23 sun ji jikkata a harin.
Nijeriya ta shafe shekaru tana fama da hare-hare daga ƙungiyoyin ‘yanta’adda da ‘yanbindiga, ciki har da ‘yan Boko Haram da ISWAP, a sassan ƙasar.
ZA KU SO WAƊANNAN











