Mai shari’a Emeka Nwite na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ya yanke wa wasu mutum huɗu hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsu da laifin kai harin ranar 5 ga Yunin 2022 a Cocin Katolika na Saint Francis da ke Owo a Jihar Ondo.
Waɗanda aka yanke wa hukuncin na cikin mutane biyar da ake tuhuma da laifukan ta’addanci guda tara da Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Nijeriya (DSS) ta shigar a kansu dangane da harin da aka kai wa cocin, inda aka kashe fiye da masu ibada 40 tare da jikkata sama da mutum 100.
Sai dai wanda ake tuhuma na biyar, Momoh Otuho Abubakar mai shekaru 47, kotun ta wanke shi tare da sallamarsa daga tuhumar.
Hukuncin ya zo ne a daidai lokacin da Nijeriya ke ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ta’addanci, wata barazana da ta daɗe tana addabar al’ummomi a sassa daban-daban na ƙasar ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.
A hukuncinsa, Mai shari’a Nwite ya same su da laifi a kan dukkan tuhume-tuhumen tara da suka shafi aikata ayyukan ta’addanci da suka saɓa wa Dokar Hana da Rigakafin Ta’addanci.
Daga cikin laifukan akwai kasancewa mambobin wata ƙungiyar ta’addanci da aka haramta, Al-Shabab (wadda aka ce tana da alaƙa da ISWAP), haɗa baki domin aikata ta’addanci, garkuwa da mutane, tsare su da kuma kashe fiye da masu ibada 40.
Mai shari’ar ya ce masu gabatar da ƙara sun tabbatar da tuhumar da ake yi wa waɗanda aka yanke wa hukunci ba tare da wata shakka ba.
Sai dai ya ce ɓangaren masu gabatar da ƙarar ya gaza tabbatar da tuhuma a kan wanda ake zargi na biyar, wanda hakan ya sa aka wanke shi.
Mutane da dama ne suka rasa rayukansu yayin da wasu da yawa suka jikkata lokacin da wasu masu ɗauke da makamai suka buɗe wa masu ibada wuta a cocin da ke hedkwatar ƙaramar hukumar Owo ta Jihar Ondo.
Lamarin ya jawo Allah-wadai daga sassa daban-daban na ƙasar, inda mutane da ƙungiyoyi suka yi kira ga gwamnati da ta kamo waɗanda suka kai harin tare da tabbatar da an hukunta su.














