| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta lashe zaɓukan cike gurbin da aka gudanar a Kano
An gudanar da zaɓukan ne a ranar Asabar domin cike guraben da aka samu sakamakon rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara: Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal).
Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta lashe zaɓukan cike gurbin da aka gudanar a Kano
'Yan takarar Jam'iyyar APC ne suka lashe zaɓen da aka gudanar a Kano / Others
13 awanni baya

Jam’iyyar APC mai mulki ta Nijeriya, ta lashe zaɓukan cike gurbi na ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kano na Ungogo da Kano Municipal.

An gudanar da zaɓukan ne a ranar Asabar domin cike guraben da aka samu sakamakon rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara: Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal).

‘Ya’yan mamatan — Aminu Sa’adu Jr. da Nabil Daneji — sun tsaya takara domin maye gurbin iyayensu a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC.

Daneji ya samu ƙuri’u 7,484 inda ya lashe kujerar mazabar Kano Municipal, kuma zai wakilci mazabar a Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen, Ibrahim Siraj, ne ya sanar da sakamakon tare da ayyana Daneji a matsayin wanda ya yi nasara.

Haka kuma, a mazabar Ungogo, ɗan takarar APC, Sa’ad, ya samu ƙuri’u 8,975 inda ya lashe kujerar.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen na mazabar, Ali Abdullahi, ya ayyana Sa’ad a matsayin wanda ya yi nasara tare da tabbatar da zaɓensa.

Kwamishinan Zaɓe na Jihar Kano na Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Abdu Zango, ya danganta ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka gani a zaɓen da yanayin lokacin da aka gudanar da shi da kuma ƙarancin shiga zaɓen daga jam’iyyun siyasa.

Da yake zantawa da ‘yan jarida yayin sa ido kan zaɓen, Zango ya bayyana cewa zaɓukan sun gudana cikin kwanciyar hankali gaba ɗaya, duk da cewa an samu ƙarancin fitowar masu zaɓe a rumfunan zaɓe da dama.

 

 

Rumbun Labarai
'Yansanda sun tabbatar da mutuwar mutum 33 a harin Kebbi
Dakarun Nijeriya sun kama mai 'kai wa Boko Haram jirage marasa matuƙa'
Mutane da dama sun rasa rayukansu a hare-haren Lakurawa a Jihar Kebbi a Nijeriya
An kashe sojoji 8 a wani harin wata ƙungiya mai alaƙa da Daesh a arewa maso gabashin Nijeriya
Tinubu ya sanya hannu kan dokar tura kuɗin man Nijeriya asusun gwamnatin tarayya kai-tsaye
Mutum 38 sun mutu sakamakon wata fashewa a wajen haƙar ma'adanai a Jihar Filaton Nijeriya
Amurka ta ƙaƙaba wa wasu 'yan Nijeriya takunkumi kan zargin ta'addanci da laifuka ta intanet
Bikin kamun kifi na Argungu: Kifin da ya kai kilogiram 59 ya ɗau hankalin dubban mutane
Sojojin Amurka sun isa arewa maso gabashin Nijeriya
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati