| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta lashe zaɓukan cike gurbin da aka gudanar a Kano
An gudanar da zaɓukan ne a ranar Asabar domin cike guraben da aka samu sakamakon rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara: Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal).
Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta lashe zaɓukan cike gurbin da aka gudanar a Kano
'Yan takarar Jam'iyyar APC ne suka lashe zaɓen da aka gudanar a Kano / Others
22 Fabrairu 2026

Jam’iyyar APC mai mulki ta Nijeriya, ta lashe zaɓukan cike gurbi na ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kano na Ungogo da Kano Municipal.

An gudanar da zaɓukan ne a ranar Asabar domin cike guraben da aka samu sakamakon rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara: Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal).

‘Ya’yan mamatan — Aminu Sa’adu Jr. da Nabil Daneji — sun tsaya takara domin maye gurbin iyayensu a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC.

Daneji ya samu ƙuri’u 7,484 inda ya lashe kujerar mazabar Kano Municipal, kuma zai wakilci mazabar a Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen, Ibrahim Siraj, ne ya sanar da sakamakon tare da ayyana Daneji a matsayin wanda ya yi nasara.

Haka kuma, a mazabar Ungogo, ɗan takarar APC, Sa’ad, ya samu ƙuri’u 8,975 inda ya lashe kujerar.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen na mazabar, Ali Abdullahi, ya ayyana Sa’ad a matsayin wanda ya yi nasara tare da tabbatar da zaɓensa.

Kwamishinan Zaɓe na Jihar Kano na Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Abdu Zango, ya danganta ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka gani a zaɓen da yanayin lokacin da aka gudanar da shi da kuma ƙarancin shiga zaɓen daga jam’iyyun siyasa.

Da yake zantawa da ‘yan jarida yayin sa ido kan zaɓen, Zango ya bayyana cewa zaɓukan sun gudana cikin kwanciyar hankali gaba ɗaya, duk da cewa an samu ƙarancin fitowar masu zaɓe a rumfunan zaɓe da dama.

 

 

Rumbun Labarai
Nijeriya na neman tallafin IMF da Bankin Duniya don rage tasirin yakin Iran kan tattalin arziki
Me ya sa hare-hare ke karu wa a Nijeriya duk da wanzuwar dakarun Amurka?
Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta soma bincike kan zargin kisan fararen-hula a kasuwar Jilli ta Yobe
ADC ta taya sabbin shugabannin jihohi murna, ta tsayar da ranar 12 ga Mayu don rantsar da su
Gwamnatin Nijeriya ta ba da umarnin soke fasfo ɗin mutanen da suka janye daga kasancewa ’yan ƙasar
Man fetur yana tsada sosai, amma mu gode wa Allah halin da muke ciki ya fi na wasu ƙasashe – Tinubu
An gano gawarwaki 61 bayan harin ta'addanci a jihar Neja ta Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda tare da ƙwace makamai a Jihar Filato
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce an kashe dakarunta a harin da Boko Haram ta kai hedkwatarsu a Borno
‘Gwarazan da ba za a iya mantawa da su ba’, Tinubu na juyayin kisan sojojin Nijeriya a harin Borno
Amurka ta bai wa jami'anta umarnin barin ofishin jakadancinta a Nijeriya saboda rashin tsaro a ƙasar
Aƙalla mutum 60 aka kashe a hare-hare daban-daban a arewa maso yammacin Nijeriya cikin mako guda
Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Nijeriya zai habaka a 2026
An mayar da 'yan Nijeriya 179 gida daga Libya
Babbar kotun Nijeriya ta ɗaure 'yanta'adda biyar
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda biyar, sun kama wanda ake zargi da garkuwa da mutane a Filato
Matatar Dangote ta ƙara man da take turawa ƙasashen Afirka yayin da yaƙin Iran ya katse jigilar mai
An buƙaci Nijeriya ta gyara yadda ake bayar da labaran rikice-rikice
An kama mutum biyar kan harbin bindiga ba bisa ƙa’ida ba da 'ya kashe' yarinya Maiduguri a Nijeriya
Abin da ya sa Kano Pillars ta lallasa Bendel Insurance da ci 4-0 — Koci