Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta lashe zaɓukan cike gurbin da aka gudanar a Kano

An gudanar da zaɓukan ne a ranar Asabar domin cike guraben da aka samu sakamakon rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara: Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal).

By
'Yan takarar Jam'iyyar APC ne suka lashe zaɓen da aka gudanar a Kano / Others

Jam’iyyar APC mai mulki ta Nijeriya, ta lashe zaɓukan cike gurbi na ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kano na Ungogo da Kano Municipal.

An gudanar da zaɓukan ne a ranar Asabar domin cike guraben da aka samu sakamakon rasuwar ‘yan majalisa biyu a watan Disambar bara: Aminu Sa’adu (Ungogo) da Sarki Aliyu (Kano Municipal).

‘Ya’yan mamatan — Aminu Sa’adu Jr. da Nabil Daneji — sun tsaya takara domin maye gurbin iyayensu a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC.

Daneji ya samu ƙuri’u 7,484 inda ya lashe kujerar mazabar Kano Municipal, kuma zai wakilci mazabar a Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen, Ibrahim Siraj, ne ya sanar da sakamakon tare da ayyana Daneji a matsayin wanda ya yi nasara.

Haka kuma, a mazabar Ungogo, ɗan takarar APC, Sa’ad, ya samu ƙuri’u 8,975 inda ya lashe kujerar.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen na mazabar, Ali Abdullahi, ya ayyana Sa’ad a matsayin wanda ya yi nasara tare da tabbatar da zaɓensa.

Kwamishinan Zaɓe na Jihar Kano na Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Abdu Zango, ya danganta ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka gani a zaɓen da yanayin lokacin da aka gudanar da shi da kuma ƙarancin shiga zaɓen daga jam’iyyun siyasa.

Da yake zantawa da ‘yan jarida yayin sa ido kan zaɓen, Zango ya bayyana cewa zaɓukan sun gudana cikin kwanciyar hankali gaba ɗaya, duk da cewa an samu ƙarancin fitowar masu zaɓe a rumfunan zaɓe da dama.