| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Ƙishirwa ta kashe mutum 49 a saharar Nijar bayan motarsu ta lalace
Mamatan na cikin waɗanda ke dawowa daga ƙasar Mali domin bukukuwan Babbar Sallah a lokacin da motarsu ta lalace sannan ruwansu ya ƙare, kamar yadda ofishin gwamnan Jihar Agadez ya bayyana a wani saƙon da ta wallafa a shafin Facebook.
Ƙishirwa ta kashe mutum 49 a saharar Nijar bayan motarsu ta lalace
Gwamnatin jihar Agadez ta ce tuni aka binne mutanen

Mutum 49 sun rasu a cikin hamadar Sahara a wani wuri a ƙasar Nijar bayan motar da ke ɗauke da su ta lalace, kamar yadda hukumomi suka bayyana ranar Alhamis.

Mamatan na cikin waɗanda ke dawowa daga ƙasar Mali domin bukukuwan Babbar Sallah a lokacin da motarsu ta lalace, sannan ruwansu ya ƙare, kamar yadda ofishin gwamnan Jihar Agadez ya bayyana a wani saƙon da ya wallafa a shafin Facebook.

Mutanen 49 “sun mutu ne sakamakon ƙishirwa a wani wuri mai nisan fiye da kilomita 80 yamma da garin Assamaka”, in ji saƙon. Assamaka wani muhimmin wurin ƙetarewa ne tsakanin Nijar da Aljeriya da Mali, ko da yakeya fi kusa da iyakar Mali.

“Bayan sun rasa ruwa kuma suka kasa gyara motarsu duk da ƙoƙarin direban da yaransa da fasinjojin, matafiyan sun sami kansu a maƙale a tsakiyar wani wuri mai wuyar sha’ani, inda yanayi mai tsanani da kuma rashin wurin samun guzuri ya sa rayuwa ta yi wahala matuƙa,” kamar yadda gwamnatin jihar ta bayyana.

Tuni dai aka binne mutanen a ƙabarin bai-ɗaya a cewar sanarwar.

Sai dai kuma mutum biyu daga cikin waɗanda suke cikin jama’ar sun tsira, bayan sun yi tafiyar fiye da kilomita 50 da ƙafa zuwa wani wuri, inda suka samu ruwa sannan kuma suka nufi Assamaka, inda mutanen biyu suka sanar da hukumomi, kamar yadda gwamnatin jihar ta bayyana.

Rumbun Labarai
Jami'an tsaro a Afirka ta Kudu sun kama masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba fiye da 200
Ƙawancen tsaro na Turkiyya da Afirka na haɓaka a tsarin duniya da ke sauyawa
Jami’an leken asiri sun lalata yunƙurin ‘yan ta’addan Daesh na kai hari a garuruwan Morroco bakwai
'Yansandan Afirka Ta Kudu sun ce mutuwar ɗan Nijeriya ba ta da alaƙa da tashin hankalin ci-rani
MDD ta yi gargaɗin cewa hare-haren RSF na iya mayar da birnin Al-Obeid na Sudan kamar Al-Fasher
Rikicin diflomasiyya ya kaure tsakanin Ghana da Afirka ta Kudu kan mutuwar ɗan Ghana
Burkina Faso, Mali da Nijar sun gabatar da sanarwar ficewa daga ICC, in ji kotun
Sojojin Mali sun raka motocin dakon mai da abinci 940 zuwa Bamako saboda fargabar harin ta'addanci
Sojojin Burkina Faso sun ce sun kashe 'yanta'adda fiye da 400 a wani hari da suka daƙile
An gurfanar da ɗalibai mata takwas a kotu a Kenya kan zargin kisan abokan karatunsu a gobara
Yadda Nijeriya ke fama da hauhawar farashin gas din girki
MDD ta yi gargaɗin cewa cutar Ebola na iya jefa kusan mutane miliyan 1 cikin talauci a DRC
Afirka ta Kudu ta mai da fiye da mutum 25000 kasashensu kafin wa'adin 30 ga Yuni na masu ƙyamar baƙi
Yadda abinci ke yin kisan mummuƙe a Afirka
Burkina Faso ta kawo ƙarshen dangantakar diflomasiyya da Faransa
Fiye da mutum 1,400 sun tsere daga jihar North Darfur ta Sudan a yini ɗaya yayin da ake zafafa yaƙi
Nijeriya da ƙasashe 4 sun ƙaddamar da sabuwar hukuma kan hanyar Abidjan zuwa Lagos ta $16bn
Nijar ta gabatar da takardar buƙatar ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya, ICC
An ci gaba da amfani da cin zarafin jinsi a matsayin makamin yaƙi a Sudan: MDD
Manyan Jami’o’in Afirka: Afirka ta Kudu ce ke kan gaba a awon matsayi na baya bayan nan