| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Saudiyya ta yaba wa sabon ƙawancen tsaron teku da ya fara aiki
Majalisar Ministocin Saudiyya ta soki ‘maimaita kai hare-hare daga Iran’ kan jiragen ruwan kasuwanci a matsayin ‘babbar karya’ dokokin ƙasa da ƙasa.
Saudiyya ta yaba wa sabon ƙawancen tsaron teku da ya fara aiki
Hotuna da aka dauka da jirgin marar matuki sun nuna jiragen ruwa a Mashigar Hormuz ka ranar 15 ga Yunin 2026. / Reuters

Majalisar Dokokin Saudiyya ta ce, fara aikin sabon ƙawancen tsaron teku na ‘Multinational Maritime Alliance’ da aka ƙaddamar ya zama "sabon mataki na haɗin gwiwa" don ƙarfafa tsaron teku.

A wani zaman da Sarkin Saudiyya Salman bin Abdulaziz ya jagoranta a Jeddah a ranar Talata, mambobin majalisar ministoci sun yi maraba da ƙaddamar da ƙawancen bayan kammala tsarin yadda zai yi aiki, in ji kamfanin dillancin labarai na Saudiyya.

"Wannan yana nuna wani sabon mataki na haɗin gwiwa don cim ma cikakken shiri na aiki," in ji majalisar ministocin a cikin wata sanarwa.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ƙawancen "inganta tsaron teku tare, zai kare 'yancin zirga-zirga a mashigai da hanyoyin ruwa, da kuma tabbatar da ci gaba da cinikayyar ƙasa da ƙasa da hanyoyin samar da kayayyaki na duniya."

Mambobin majalisar ministocin sun kuma yi Allah wadai da abin da suka bayyana a matsayin "hare-haren da Iran ta kai" kan jiragen ruwa na kasuwanci a matsayin "mummunan keta dokokin ƙasa da ƙasa."

A ranar 30 ga Yuli, Saudiyya, tare da wasu ƙasashe 13, sun bayyana shirye-shiryen kafa ƙawancen haɗin gwiwa a teku, wanda ke da nufin tabbatar da hanyoyin ciniki da makamashi ta cikin Tekun Bahar Maliya, Tekun Aden, da kuma Mashigar Bab al Mandeb.

A farkon wannan watan, an naɗa Admiral Abdullah bin Salem Al-Shehri a matsayin kwamandan sabon ƙawancen.