| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Yaƙin Yemen ya raba fiye da mutum 100,000 da muhallansu — Majalisar Ɗinkin Duniya
Hukumar ta ce fadan ya raba iyalai da muhallansu a wani faɗin yanki, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin cewa za a iya samun ƙarin gudun hijira a cikin Yemen da kuma ƙarin kwararar ’yan gudun hijira idan rikicin ya ƙara tsananta.
Yaƙin Yemen ya raba fiye da mutum 100,000 da muhallansu — Majalisar Ɗinkin Duniya
Yaƙin Yemen ya raba fiye da mutum 100,000 da muhallansu — Majalisar Ɗinkin Duniya

Ƙara tsanantar faɗa tsakanin dakarun gwamnatin Yemen da ƙungiyar Houthi ya tilasta wa fiye da mutane 100,000 barin gidajensu a cikin ƙasar, yayin da wasu dubban mutane suka tsere zuwa ƙasashen waje, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

Dubban mutane sun tsere daga gidajensu sakamakon hare-haren da Houthi ta shafe mako guda tana kaiwa, waɗanda suka ƙare da ƙungiyar ta kwace ragowar gabar tekun Bahar Maliya ta Yemen tare da ƙara ƙarfafa ikonta kan Mashigar Bab al-Mandab.

Mashigar ta ƙara zama mai muhimmanci yayin da yaƙin Amurka da Iran ke kawo cikas ga zirga-zirgar jiragen ruwa ta Mashigar Hormuz.

Hukumar kula da ’yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) ta yi gargadi a cikin wata sanarwa a ranar Talata cewa:

“Ƙara tsanantar tashin hankali cikin sauri a gabar tekun yammacin Yemen ya raba sama da mutane 100,000 da muhallansu a cikin ƙasar, tare da tilasta wa wasu dubban mutane neman mafaka” a ƙasar Djibouti.

Hukumar ta ce fadan ya raba iyalai da muhallansu a wani faɗin yanki, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin cewa za a iya samun ƙarin gudun hijira a cikin Yemen da kuma ƙarin kwararar ’yan gudun hijira idan rikicin ya ƙara tsananta.

UNHCR ta ce fiye da mutane 2,400 sun tsallaka teku daga Yemen zuwa Djibouti cikin kwanaki huɗu kacal da suka gabata, inda mata, yara da tsofaffi suka kasance sama da kashi 60 cikin 100 na waɗanda suka isa.

Sandrine Desamours, wakiliyar UNHCR a Djibouti, ta ce:

“Mutane na isa bayan sun yi doguwar tafiyar teku mai wahala. Da yawa daga cikinsu sun gaji, sun shiga damuwa, kuma suna ɗauke da kaɗan daga cikin abubuwan da suka iya kwaso.”

“Taimakon da ake bayarwa ya riga ya shiga matsala. Muna matuƙar buƙatar ƙarin tallafi cikin gaggawa kafin ƙarin iyalai su iso.”

UNHCR ta ce iyalan da suka rasa matsugunansu a cikin Yemen sun tsere cikin gaggawa, ba tare da sun samu damar kwashe kayayyaki da yawa ba. Wannan ya ƙara nuna buƙatar samar da matsuguni, abinci, ruwan sha mai tsafta, kiwon lafiya da ayyukan kariya.

Hukumar ta kuma bayyana damuwa kan ƙarin haɗarin da sama da ’yan gudun hijira da masu neman mafaka 65,000 da aka yi wa rajista a Yemen ke fuskanta, galibinsu daga Somaliya da Habasha.

Ta ce samun damar kai agajin jinƙai ga waɗanda abin ya shafa na ci gaba da kasancewa babban ƙalubale.

A cewar hukumar:

“Rashin tsaro, lalacewar hanyoyi, katsewar hanyoyin sadarwa da takaita zirga-zirga na kawo cikas ga ayyukanmu.”

Ƙara tsanantar rikicin ta kuma haifar da damuwa game da tasirinsa kan jigilar kayayyakin agajin jinƙai a duniya, wadda tuni ke fuskantar matsin lamba sakamakon ci gaba da samun cikas a yankin Mashigar Hormuz.

UNHCR ta ce ci gaba da rashin tsaro a kusa da Mashigar Bab al-Mandab, wadda muhimmiyar hanyar sufuri ce ta teku da ta haɗa Bahar Maliya da Tekun Aden, na iya shafar jigilar kayayyakin agaji da na kasuwanci zuwa Yemen, Sudan da sauran wuraren da ake fama da matsalolin jinƙai a yankin da ma wajensa.

Rumbun Labarai
Isra’ila ta sake jaddada barazanar kai hari wuraren makamashin Iran
Ƙin amincewar Ingila da mamayar da Isra’ila ke yi ba bisa doka ba ya kawo babban sauyi- Wani Malami
Trump ya ce Amurka tana samun nasara a kan Iran kuma za ta kira Mashigar Hormuz da 'Mashigar Trump'
Iran ta kai hari kan sansanin sojoji da jiragen yaƙin Amurka da ke Jordan
Ministocin Larabawa sun yi watsi da shirin korar Falasdinawa, suna neman a kare Gaza
Iran ta yi gargadin cewa matsin lambar Amurka na iya sakawa a hana jiragen ruwa shiga tekun Gulf
Masu aikin Umrah biyu sun rasu, 25 sun jikkata bayan bas ɗauke da 'yan ƙasar Masar ta yi hatsari
Dalilan da suka sa ya kamata Uganda ta sake tunani kan tura dakaru Gaza
Jaridar Isra'ila ta ba da shawarar yafe wa matasan Amurka bashi don su shiga yaƙin Iran
Ben-Givir na Isra'ila ya gabatar da shirinsa na korar Falasɗinawa 1.8m daga Gaza a shekara bakwai
Trump na duba yiwuwar ayyana kawo ƙarshen yaƙi da Iran
Amurka na yaƙar Iran ne don kare ƙawayenta a Gabas ta Tsakiya da ƙasashen Yamma - Trump
Iran ta ce harin bam na Amurka a wajen bikin aure a Hormozgan ya kashe fararen hula
Kakakin Majalisar Dokokin Iran ya buƙaci ’yan kasa su rage amfani da fetur
Iran ta ce ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke UAE, ta harbo jiragen leken asiri na ƙasar
Harin Amurka a Tsibirin Larak na Iran ya kashe mutane da dama da kuma jikkata wasu
Karshen ayyukan 'yan ta'addar PKK/YPG
Yarjejeniyar Makka na aike wa da 'Saƙon haɗin kai da zaman lafiya': Firaministan Pakistan
Shugaban Siriya ya naɗa tsohon shugaban ƙungiyar SDF/YPG a matsayin mai ba shi shawara
Babbar ɗimuwar Netanyahu: Mafarkin Turkiyya na shirin kai hari