| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Nijar na son ƙara adadin jihohinta daga 8 zuwa 19 da kuma sauya sunayen wasu jihohim
Sabbin jihohin za a samar da su ne daga cikin jihohi takwas da ƙasar ke da su a halin yanzu.
Nijar na son ƙara adadin jihohinta daga 8 zuwa 19 da kuma sauya sunayen wasu jihohim
NIjar za ta ƙara yawan jihohinta daga takwas zuwa 19 / ANP

Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida da Tsaro ta Nijar ta gabatar da wani sabon daftarin dokar sake fasalin rabon yankunan ƙasar, wanda zai ƙara adadin jihohin Nijar daga takwas zuwa 19.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar, ANP ya ruwaito cewa shirin ya kuma tanadi ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 20 domin ƙarfafa kasancewar gwamnati a faɗin ƙasar da kuma inganta shugabanci a matakin ƙananan hukumomi.

A cewar gwamnatin ƙasar, sabon tsarin zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki da walwalar jama’a, tare da inganta ayyukan tsaro da gudanar da harkokin gwamnati bisa la’akari da ƙalubalen tsaro da ci gaban al’umma.

Wannan sauyi na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin mulkin sojin Nijar ke ci gaba da aiwatar da sauye-sauye a tsarin mulki da gudanarwar ƙasar tun bayan hambarar da gwamnatin farar hula a watan Yulin 2023.

Bisa ga sabon tsarin, jihohin Agadez da Diffa da Dosso za su samar da jihohi biyu-biyu, yayin da jihohin Maradi da Tahoua da Tillabéri da Zinder kowacce za ta samar da jihohi uku. Sai dai Yamai ce kaɗai za ta ci gaba da kasancewa jiha guda ɗaya.

Baya ga ƙirƙirar sabbin jihohi, gwamnatin Nijar ta kuma sauya sunayen tsoffin jihohi takwas na ƙasar.

A ƙarƙashin sabon tsarin:
Diffa za ta koma Komadougou
Zinder za ta koma Damagaram
Maradi za ta koma Katsina
Dosso za ta koma Ziggui
Tillabéri za ta koma Issa
Agadez za ta koma Abzine
Tahoua za ta koma Ader

Sai dai Yamai ce kaɗai za ta ci gaba da amfani da tsohon sunanta.

Sauran sabbin jihohin da za a ƙirƙira sun haɗa da Kawar da Mangari da Arewa da Tazar da Gobir da Azawak da Magia da Tougana da Kourfey da Daoura da Damergou.

Wasu daga cikin sababbin sunayen jihohin sun samo asali ne daga tsoffin masarautu da yankunan tarihi da suka yi fice a Nijar tun kafin mulkin mallaka.

Haka kuma, daftarin dokar ya tanadi ƙirƙirar sabbin manyan biranen jihohi 15 da kuma sabbin ƙananan hukumomi 20, ciki har da Tabelot da Djado da Chétimari da Dogon Kiria da Guéchémé da Sambéra da Tibiri da Ourafane da Kornaka da Kanambakaché da Hamdallaye da Bambèye da Kaou da Ourno da Tamaské da Goroual da Makalondi da Kellé da Gangara da Guidimouni.

Rahoton ya ce sabbin ƙananan hukumomin za su rabu tsakanin jihohin ƙasar daban-daban, inda Maradi da Tahoua za su samu huɗu-huɗu, Dosso da Zinder uku-uku, Agadez da Tillabéri biyu-biyu, yayin da Diffa da Yamai za su samu guda ɗaya kowacce.

Wannan sauyi na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin mulkin sojin Nijar ke ci gaba da aiwatar da sauye-sauye a tsarin mulki da gudanarwar ƙasar tun bayan hambarar da gwamnatin farar hula a watan Yulin 2023.

Nijar dai na fama da hare-haren ‘yanta’adda musamman a yankunan Tillabéri da Diffa da Tahoua, lamarin da hukumomi ke cewa sabon tsarin gudanarwa zai taimaka wajen ƙara kusantar gwamnati da jami’an tsaro zuwa yankunan karkara.

Masu lura da al’amura na ganin sauyin na daga cikin manyan gyare-gyaren tsarin gudanarwa da Nijar ta yi cikin shekaru da dama.

Rumbun Labarai
Mali ta haramta hawa babura a wajen birane saboda hare-haren ta'addanci
Tawagar kwallon DRC na neman abokiyar karawa bayan Sifaniya ta fasa buga wasa da su saboda Ebola
'Yan Nijeriya da Mozambique da Laberiya na cikin mutum  21 da gobarar otel ta kashe a New Delhi
Shugaban Nijar Abdourahamane Tiani ya fara ziyarar aiki a Turkiyya
Nijar da Benin sun ƙaddamar da kwamitin da zai sa ido kan iyakokin ƙasashen biyu
Manyan attajiran Afirka da kuma nauyin talaucin da nahiyar ke fama da shi
Malawi za ta kwashe 'yan ƙasarta daga Afirka ta Kudu saboda matsalar rikicin ƙyamar baƙi
Dalibai tara sun gurfana a gaban kotu kan tayar da gobara a wata makaranta a Kenya
Mutane da yawa sun fito da wuri don kaɗa kuri'a a babban zaben Habasha
Shugaban WHO ya ziyarci cibiyar Ebola yayin da cutar ke ƙara ƙamari
Amurka ta aike wa Nijar kayan aikin soja da darajarsu ta kai dala miliyan 2.3 duk da takun-saƙa
Ɗalibai 16 sun rasu sakamakon gobara a wata makarantar 'yanmata a Kenya
Ghana ta kwashe 'yan ƙasarta 300 daga Afirka ta kudu yayin da ake zanga-zanga kan baƙin haure
Mutane uku sun mutu bayan motar fasinja ta yi karo da giwa a gandun dajin Uganda
Shugaban Senegal Faye ya naɗa sabon firaminista da zai maye gurbin Sonko
Adadin mutanen da Ebola ta kashe a Jamuhuriyar Kongo ya wuce 200
Shugaban Senegal Faye ya sallami Firaministansa Ousmane Sonko
Kenya za ta rage farashin man dizel bayan zanga-zangar da aka yi kan tsadar makamashi
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar za ta ƙayyade kuɗin gidajen haya
Sierra Leone ta amince ta karɓi kashin farko na waɗanda aka taso ƙeyarsu daga Amurka