An sake tilasta wa sojojin Isra'ila su tabbatar da abin da za su so su bayyana. Wani hoto da aka watsa a yanar gizo a ranar 6 ga Mayu ya nuna wani sojan Isra'ila yana riƙe da taba sigari a bakin butum-butumin Nana Maryam a Debel, wani ƙauye da ke kudancin Lebanon.
Mai magana da yawun rundunar ya ce sojoji "suna kallon lamarin da matuƙar tsanani" kuma cewa halayen sojan "ya bambanta da ƙimar da ake tsammani daga ma'aikatan rundunar."
Wannan dai, shi ne kalami ɗaya ce da Isra'ila ta fitar ƙasa da makonni uku da suka gabata lokacin da aka ɗauki hoton wani soja yana lalata butum-butumin Yesu, shi ma a Lebanon.
Kalaman Allah wadai daga mahukunta ya zama al'ada; ana iya faɗi, ba komai, kuma yana ƙara zama abin da ba zai gamsar da al'ummomin Kirista ba idan suka kalli wani tsari da ke faruwa a faɗin Lebanon da ma wasu wurare.
Ga wasu ƙwararru, ba za a iya raba cin zarafin alamomin Kirista da wurare akai-akai daga tushen akidar da ke ƙarƙashin halayen Isra'ila a yankin ba.
"Akidar kafa kasar Yahudu wata alama ce ta mulkin mallaka na 'yan gudun hijira kuma tana bayyana a cikin wariyar launin fata; rabuwa, nuna bambanci, da kuma raba kan jama'a. Zai iya faɗaɗa ne kawai ta hanyar tsarkake ƙabilanci da kuma, inda ya cancanta, kisan kare dangi," a cewar Stephen Sizer, ƙwararre kan addinin Kirista kuma tsohon jami’i a Cocin Ingila.
"Kasancewar mutanen ‘yan asalin yanki, waɗanda ake ganin makaskanta ne, matsala ce. Cin zarafin ƙabilarsu yana tare da ɓata duk wani abu da suke ɗauka da muhimmanci, kamar addininsu," Sizer ya fada wa TRT World.
"Saboda haka ba abin mamaki ba ne cewa yayin da Isra'ila ke da'awar karewa da girmama 'yancin addini, a zahiri, ta shafe fiye da ƙarni ɗaya tana lalata wuraren ibada na Musulmi da Kirista," in ji shi.
Sabon bidiyon lalata wuraren ibada d alamomin addini da sojojin Isra'ila suka yi ya bayyana ƙasa da wata guda bayan an ɗauki wani sojan Isra'ila yana fasa butum-butumin Yesu a Debel, wani ƙauyen Kiristoci a kudancin Lebanon.
Bayan abin da ya faru a baya game da mutum-mutumin Yesu, an janye sojan da ya fasa butum-butumin da kuma sojan da ya ɗauki hotonsa daga fagen yaƙi kuma an yanke musu hukuncin ɗaurin kwanaki 30 a gidan yarin soja.
Sauran sojoji shida waɗanda suka shaida hakan kuma ba su yi komai ba sun fuskanci matakin ladabtarwa kawai, martanin da masu suka suka kira bai dace ba ga wani aiki da ya jawo fushin duniya.
A cikin wata sanarwa da Babban Limamamin Coci Pierbattista Pizzaballa ya sanya wa hannu, Majalisar Dokokin Katolika ta Ƙasa Mai Tsarki ta bayyana "baƙin cikinta da kuma Allah wadai," inda ta bayyana wannan aiki a matsayin "mummunan cin zarafi ga addinin Kirista wanda ke janyo ƙarin wasu rahotannin ɓata alamomin Kirista da sojojin Isra’ila ke yi a kudancin Lebanon."
Majalisar ta ce lamarin ya nuna "rashin nasara a cikin ɗabi'a da kuma tsarin ɗan adam inda har ma da mafi girman rashin girmamawa ga wurare masu tsarki da kuma cin zarafin darajar wasu ma su daraja."
Shugabannin Yahudawa sama da 150 daga ƙungiyoyi daban-daban a duniya suma sun sanya hannu kan wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ke Allah wadai da wannan aiki, suna kiran sa "wani mummunan zagi, ɓata sunan Allah," tare da neman afuwa ga al'ummar Kirista na duniya.
"A cikin yaƙe-yaƙen dariku da na addini da ake ci gaba da yi a Gabas ta Tsakiya da yankin Arewacin Afirka, ƙananan al'ummomin Kirista ne masu rauni waɗanda suka fuskanci mafi munin hare-haren," a cewar Farfesa Amalendu Misra, masanin Siyasar Duniya a Jami'ar Lancaster, kuma ƙwararre kan tsattsauran ra'ayin addini.
"Abin mamaki ne musamman ganin cewa an haifi Kiristanci a nan kuma an yi riko yawancin wayewar kai da al'adun wannan addini mai ƙarfi sosai," in ji Misra ga TRT World.
Ya ƙara da cewa, "Babban rashi ga al'ummar duniya shi ne lalata tsoffin wuraren ibada na Kiristanci da kuma alamomin da suka fi muhimmanci a ƙasar da ta samo asali sama da shekaru dubu biyu da suka gabata."
Bayyanannen salo
Tsakanin al’amuran cin zarafin da suka faru guda biyu, wani lamari ya ƙara ta'azzara hoton.
Sojojin Isra'ila sun amsa cewa sun yi barna ga wani gini a cikin harabar wani gidan ibada na Katolika kusa da ƙauyen Yaroun a kudancin Lebanon, kodayake sun musanta girman ginin, suna da'awar cewa a ginin "babu wata alama ta waje da ke nuna cewa wajen ibadar wani addini ne".
Cocin Katolika da ke Lebanon ta yi watsi da salon karya na sojoji. "Waɗannan ba sansanonin soja ba ne. Waɗannan wurare ne na yaɗa zaman lafiya, soyayya da ilimi," in ji Abdo Abou Kassm, daraktan Cibiyar Bayanai ta Katolika.
Abubuwan nuna tsana da suka faru a cikin makonnin da suka gabata sun kasance masu tsanani kuma aikin tsirarun masu tsattsauran ra'ayi ne, a cewar William Shomali, Babban Limamin Kudus da Falasɗinu.
"Ɗaya daga cikin mafi munin abin da ya faru kwanan nan, shi ne cin zarafin da aka yi wa wata mata 'yar Katolika 'yar Faransa wacce ke tafiya kusa da ɗakin sama, a wajen da ba shi da nisa daga kabarin annabi Dauda," Shomali ya shaida wa TRT World.
"Abin da ya kamata a yi shi ne a ilmantar da waɗannan tsirarun masu tsaurin ra'ayi su girmama alamomin Kirista da Musulmi tunda Ƙasa Mai Tsarki ta ƙunshi addinai uku," in ji shi.
Abubuwan da suka faru a Debel da Yaroun ba su tsaya haka ba. A lokacin hare-haren da Isra'ila ta kai a baya a Lebanon a bazarar 2024, sojoji sun dauki hoton kansu suna lalata wani gidan ibada a Deir Mimas, da kuma wani butum-butumin Wali George da ke Yaroun.
A watan Yulin 2025, a wani hari da Isra'ila ta kai kan harabar Cocin ‘Holy Family’ da ke Gaza, cocin Katolika daya tilo da ke yankin, ta kashe tare da raunata fararen hula wadanda suka nemi mafaka a ciki.
A harabar Cocin Wali Porphyrius, daya daga cikin tsoffin majami'u a yankin, hare-haren Isra'ila sun haifar da mace-mace da raunuka yayin da fararen hula suka nemi mafaka a wajen.
A cewar Cibiyar Tattara Bayanai ta 'Yancin Addini, wata kungiya da ke zaune a Kudus, an kiyasta cewa an samu cin zarafi 181 da aka kai wa Kiristoci, alamomin Kirista, da cibiyoyin Kirista a Isra'ila a shekarar 2025 kadai, tare da karin wasu 44 tsakanin Janairu da Maris din 2026.
"Akwai girmamawa mai zurfi a cikin al'ummomin Musulmi da Kirista, da kuma tsakanin Yahudawa masu adawa da akidar Zionism, ga al'adun addinin juna, tare da fahimtar cewa rayuwa cikin zaman lafiya da tsaro yt kunshi kaunar maƙwabtanmu, babban abin da ya zama wajibi ga Kiristoci," in ji Sizer.
“Masu akidar Zionism a iya amfani da raba kawunansu ku mulke su, amma a zahiri, hadin kai, misali tsakanin Falasdinawa Musulmi da Kirista, ya fi girma yanzu fiye da da."
"'Yan Lebanon sun san dabi'un nuna wariyar launin fata da ke tattare da masu akidar Zionism, wadanda aka gani a zahiri a cikin lalata kauyukan Lebanon da ke kudancin Beirut," in ji Sizer.
Neman afuwa ba tare da daukar mataki ba
Martanin ƙasashen duniya ya ƙaru sosai a duk lokacin da Isra'ila ta kai hari kan alamomin addini, amma abin da ba a gani a tattaunawar ƙasashen duniya shi ne daukar wani kwakkwaran mataki da bayyana a gaban shari’a.
A ƙarƙashin Yarjejeniyar Hague ta 1954 don Kare Kayan Al'adu idan aka yi rikici, wanda Isra'ila ke cikinta, an haramta lalata ko rashin girmama kayan al'adu da na addini da gangan.
Uzuri da hukuncin ɗaurin kurkuku na kwanaki 30 ga sojoji ba su zama babban hukunci na shari'a da yarjejeniyar ta hasato ba.
Dokar ƙasa da ƙasa ta bayyana sarai game da haƙƙin al'ummomi masu addini da wuraren ibadarsu, a cewar Farfesa Misra.
"Kasashe na da tabbatar da ɗabi'a, ɗabi'a da na shari'a game da kare ƙungiyoyin addinai da kayayyakin al'adun addininsu, alamomi da abubuwan tarihi na ibada," in ji Misra.
"Yawancin wuraren gine-gine na Yahudawa, Kirista da Musulunci da wuraren ibada a Gabas ta Tsakiya suna cikin kayan tarihi na ɗan adam da UNESCO ta amince da su."
"Duk wani karfi ko hukumar gudanarwa da ke lalata ko rusa waɗannan al'adu na addini da al'adun gargajiya da gangan, to na aikata laifukan da suka saba wa ɗabi'a da jinkai waɗanda ba su da hujja a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa na yanzu," in ji shi.
Debel, ƙauyen Kiristocin Maronite mai nisan kilomita biyar daga kan iyakar Isra'ila, yana cikin ƙauyukan Kiristoci da Isra'ila ta keɓe daga umarnin gudun hijira, wanda hakan ya sa rashin da'a na sojojinta da ke can ya fi bayyana kuma yana da wahalar a yi watsi da shi.
Lokacin da rikici ya ci gaba da faruwa a ƙauyen kuma a kan al'ummar Kirista, Isra'ila ta yi iƙirarin cewa sun tsira daga "hare-haren soja", amma maimaita cin zarafin ya lalata wannan kalami.
Ya kamata a bayyana tasirin hakan, a cewar Sizer.
"Ya kamata a yi watsi da akidar Zionism, a matsayin nau'in wariyar launin fata, a ƙasashen duniya kuma a kore shi daga Majalisar Dinkin Duniya, yayin da ya kamata a kama shugabannin akidar da jami'anta a tuhume su da laifukan yaƙi," in ji shi.
















