GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Abubuwan da muka sani game da martanin Hamas kan shirin Trump a Gaza
Hamas ta amince ta saki dukkan Isra'ilawa da ke hannunta, waɗanda suke a raye da waɗanda suka mutu, a ƙarƙashin shawarwarin shugaban Amurka Trump game da Gaza sannan ta ce a shirye take ta shiga yarjejeniyar tsagaita wuta nan-take.
Abubuwan da muka sani game da martanin Hamas kan shirin Trump a Gaza
Hamas izražava "zahvalnost" za arapske, islamske i međunarodne posredničke napore, uključujući one koje predvodi Trump.
4 Oktoba 2025

Ƙungiyar gwagwarmaya ta Hamas da ke Falasɗinu ta mayar da martani a hukumance game da daftarin shawarwari na shugaban Amurka Donald Trump game da yankin Gaza.

Wakilan ƙasashen Qatar da na Falasɗinu sun bayyana cewa Hamas ta nemi ƙarin haske game da wasu saɗarori da ke cikin ƙudurin amma ta ƙara da cewa a shirye take ta shiga tattaunawar tsagaita wuta ta hannun masu shiga tsakani.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta amince ta saki dukkan Isra'ilawa da ke hannunta, waɗanda suke a raye da waɗanda suka mutu, kamar yadda Trump ya bayar da shawara.

Sai dai wani babban jami’in Hamas ya shaida wa Al Jazeera cewa miƙa mutanen cikin awanni 72, kamar yadda aka bayar da shawara, abu ne "da ba zai yiwu ba".

Hamas ta jaddada amincewarta ta miƙa harkokin gudanarwa na Gaza ga wata hukuma ta ƙwararru ta Falasɗinawa, inda ta ƙara da cewa dole ne duk wani shiri game da makomar Gaza ya kasance cikin “babban tsari na ci-gaban ƙasar” wanda zai ƙunshi dukkan ɓangarorin Falasɗinu da ba sa ga maciji da juna sannan a gina shi bisa dokokin ƙasashen duniya.

Hamas ta miƙa "godiya" ga Larabawa da ƙasashen Musulmai da sauran ƙasashen duniya game da ƙoƙarinsu na tabbatar da tsagaita wuta, ciki har wanda Trump ya jagoranta.

Hamas ta ja hankali game da wata saɗara a cikin ƙudurin na Trump da ke magana game da “makomar Zirin Gaza da kuma ‘yancin al’ummar Falasɗinu" tana mai cewa kamata ya yi "dukkan ‘yan ƙasa da kuma dokokin ƙasashen duniya" su kasance waɗanda za su samar da makomar yankin.

Rumbun Labarai
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana