| Hausa
TURKIYYA
3 minti karatu
Lokaci ya yi da ya kamata kowa ya ɗauki alhakin tasirin sauyin yanayi yadda ya dace: Emine Erdogan
Uwargidan shugaban kasar Turkiyya ta soki gazawar tsarin duniya na raba nauyin tasirin sauyin yanayi daidai-wa-daida, inda ta yi kira da a hada kai a ƙawancen da ke ba da fifiko ga tausayi da daidaito domin yakar kalubalen yanayi yadda ya kamata
Lokaci ya yi da ya kamata kowa ya ɗauki alhakin tasirin sauyin yanayi yadda ya dace: Emine Erdogan
Emine Erdogan addressing the Vatican’s Pontifical Academy of Social Sciences. / Turkish Presidency
3 Yuli 2025

Yayin da gobarar daji take ta kamawa a kasashe daban-daban a duniya, Uwargidan Shugaban Kasar Turkiyya, Emine Erdogan, ta yi kira ga kasashe masu arziki su raba nauyin matsalar sauyin yanayi cikin adalci da daidaito.

Ta nuna yadda sauyin yanayi ke shafar kasashe masu tasowa fiye da ƙima, inda ta ce wasu kasashe, duk da cewa ba su kai kashi 1 cikin 100 na samar da hayakin da ke gurbata yanayi ba, suna fuskantar mummunan sakamako kamar zama 'yan gudun hijirar yanayi, sannan suna rasa muhimman albarkatun abinci.

“Kasashe ba za su iya fuskantar matsaloli da yawa su kadai ba,” in ji ta, yayin da take kira ga hadin gwiwar kasa da kasa don magance wannan rashin daidaito, a yayin jawabin da ta gabatar a Majami’ar Vatican ta Pontifical Academy of Social Sciences.

Ta jaddada bukatar daukar matakan gaggawa kan sauyin yanayi da kuma Muhimmin Shirin Zero Waste na Turkiyya, tana bayyana su a matsayin matakai masu muhimmanci wajen tabbatar da adalci da dorewa ga makomar bil'adama gaba daya.

Ta soki yadda tsarin duniya ya kasa raba nauyin matsalolin cikin daidaito, tana kira ga kafa kawance masu ma'ana da suka fifita tausayi da adalci don magance kalubalen yanayi yadda ya kamata.

Babban abin da ta mayar da hankali a jawabin nata shi ne Shirin Zero Waste na Turkiyya, wanda aka kaddamar a shekarar 2017, wanda ya zama wani shiri na duniya ta hanyar kudurin Majalisar Dinkin Duniya.

Erdogan ta bayyana shirin a matsayin wanda aka gina bisa “aminci ga bil'adama” da kuma sadaukarwa ga adalcin tsakanin al'ummomi da tsararraki. \

“Muna kallon wannan ba kawai a matsayin nauyin muhalli ba, amma a matsayin gwajin tabbatar da adalci tsakanin al'ummomi da tsararraki,” in ji ta.

Shirin ya nuna yadda Turkiyya ke ganin yanayi a matsayin amana daga Allah, wanda ke bukatar tunani mai zurfi.

Misis Erdogan ta jaddada cewa hada fasaha da ka'idojin dabi'a na iya kawo mafita mai sauyi, wanda zai tabbatar da cewa alkawuran duniya sun zama aiki mai ma'ana. Ta gargadi cewa ba tare da girmama yanayi ba, alkawuran yanayi na iya zama “kama a cikin rubuce-rubuce kawai.”

Shirin Zero Waste, a cewarta, yana nuna yadda nauyin muhalli zai iya hade da adalcin zamantakewa, ta hanyar rage sharar gida da kuma inganta dabi'un dorewa a duniya baki daya.

Erdogan ta yi kira ga sauyin tunani da ta jaddada bukatar sake fasalta dangantakar bil'adama da duniya don cimma ci gaban muhalli mai dorewa. Ta danganta matsalar sauyin yanayi da batutuwa kamar talauci, hijira, da rashin daidaito.

Ta kawo alkaluma masu tayar da hankali, ciki har da mutum biliyan uku da ke rayuwa da kasa da dala 5.50 a kullum da kuma 'yan gudun hijira miliyan 70, don nuna irin tasirin da gazawar tsarin duniya ke yi ga mutane.

Wadannan kalubale, a cewarta, suna bukatar mafita ta hadin kai da aka gina bisa hadin kai, tare da daukar matakan yanayi a matsayin ginshikin gina duniya mai adalci.

UWargidan Erdogan ta jaddada jagorancin Turkiyya a kokarin jinƙai da muhalli, tana nuna yadda kasar ke karbar bakuncin kusan 'yan gudun hijira miliyan hudu da kuma ayyukan tallafinta na duniya.

Rumbun Labarai
Kare gaskiya na da matuƙar muhimmanci a 'zamanin labaran ƙarya': Daraktan Sadarwa na Turkiyya
An fara taron Stratcom 2026 a Istanbul yayin da hankalin duniya ke ƙara tashi da yaƙin watsa labarai
Baya ga warware rikice-rikice, Turkiyya na sauya yadda al’amura ke gudana a duniya
Fidan na Turkiyya ya yi jerin tattaunawa da takwarorinsa kan kokarin kawo karshen yakin Iran
Ƙasashen Gulf za su iya ‘ɗaukar mataki’ kuma yaƙin Iran yana iya watsuwa: Babban jami'in Turkiyya
China ta yaba wa Turkiyya, Saudiyya, Qatar kan rawa a tsagaita wuta tsakanin Pakistan da Afghanistan
Shugaba Erdogan ya girmama nasarar 'Canakkale' a yaƙin duniya na ɗaya
Tallafin NATO ga Turkiyya zai gwada ƙarfin ƙawancensu yayin tashin hankalin Gabas ta Tsakiya: masana
An daƙile makami mai linzami na Iran a kan hanyarsa ta kutsawa Turkiyya
Turkiyya ta tura jiragen yaƙi na F-16 shida Arewacin Cyprus yayin yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran
Turkiyya ta kira jakadan Iran, ta nuna damuwarta kan harba makami mai linzami a sararin samaniyarta
NATO ta kakkaɓo makami mai linzami na Iran da aka harba Turkiyya
Shugaba Erdogan ya koka da rushewar tsarin tafiyar da duniya da ke aiki bisa doron dokoki
Hari kan Iran “zalunci ne kuma ba bisa ka’ida ba”, in ji jam’iyya mai mulkin Türkiyya
Shugaba Erdogan ya yi kira kan a yi amfani da diflomasiyya yayin da rikicin Iran ke rincaɓewa
Turkiyya ta yi kira ga Amurka, Isra'ila da Iran su tsagaita wuta nan-take
Ankara ta samar da shafin intanet kan taron COP31 na sauyin yanayi da za a gudanar a Turkiyya
Pakistan da Turkiyya sun yi alƙawarin zurfafa alaƙar tsaro a ziyarar manyan jami'ai zuwa Ankara
Shugaba Erdogan ya miƙa saƙon 'Barka da Azumi' ga ƙasarsa da duniyar Musulmai
Erdogan: Amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland ba za ta amfani kowa ba