An ba ɗaya daga cikin jirage ruwan Turkiyya izinin wucewa ta Mashigar Hormuz, in ji Ministan ƙasar
Ma'aikatar sufuri ta Turkiyya ta ce an ba wa ɗaya daga cikin jiragen ruwan ƙasar 15 izinin wucewa ta mashigar Hormuz, inda ta ƙara da cewa jiragen ruwan suna da jimillar ma'aikata 171 a yankin.
An ba wa wani jirgin ruwa mallaƙin Turkiyya da ke jira kusa da Iran izinin wucewa ta hanyar mashigar Hormuz bayan da hukumomi suka sami izini daga Tehran, in ji Ministan Sufuri da abubuwan more rayuwa na Turkiyya Abdulkadir Uraloglu.
A zantawar da ya yi da kafofin watsa labarai na Turkiyya a ranar Alhamis wanda aka fitar ranar Jumma'a, Uraloglu ya ce Ankara ta ja hankali tare da gargadin tsaro mafi girma game da mashigar, sannan ta ci gaba da tuntuɓar jami'an Iran game da yanayin sauran jiragen ruwa 14 mallakar Turkiyya da ke can.
"Jirage 15 (waɗanda ke dauke da tambarin sunan Turkiyya a jikinsu) suna nan; mun samu izinin wucewar ɗaya daga cikinsu daga hukumomin Iran, wanda ya yi amfani da hanyar tashar jiragen ruwan Iran, kuma ya wuce," in ji Uraloglu.
Ma'aikatar ta ce jirgin Turkiyya ƙirar Rozana ne ya samu damar wucewa ta mashigar, ta kuma ƙara da cewa jimillar ma'aikatan jiragen ruwan Turkiyya a yankin guda 171 ne.
Yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran ne ya haifar da rufe Mashigar Hormuz, yanayin da ya bar tankunan mai da sauran jiragen ruwa a maƙale, lamarin da ya haifar da damuwa game da samar da makamashi a duniya.
A ɓangare guda kuma, ma'aikatar ta ce jiragen saman Turkiyya da na Ajet sun soke tashin jiragensu zuwa Iraki, Siriya, Lebanon, Jordan, Doha, Dubai, Abu Dhabi, Kuwait, Bahrain da Dammam har zuwa 19 ga watan Maris, kazalika an soke tashin jirage zuwa Iran har zuwa 20 ga Maris.
Haka kamfanin Pegasus Airlines shi ma ya soke jigilar jiragensa zuwa Kuwait, Bahrain, Doha, Amman, Beirut, Iraq, Dubai, Abu Dhabi da Sharjah har zuwa 23 ga watan Maris, yayin da ya soke tashin jirage zuwa Iran har zuwa 28 ga Maris.
Kazalika Turkish Airlines ya kara Oman a cikin jiragensa da ya soke jigilarsu, in ji shi, inda ya kara da cewa an karkatar da jirage 76 zuwa Turkiyya tun lokacin da aka fara yakin a ranar 28 ga Fabrairu.