| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Dimokuraɗiyyar Afirka: Ana zaɓen shugaban ƙasa a Sao Tome and Principe
Masharhanta sun bayyana tsibirin mai mutane 200,000 a matsayin abin koyi na dimokuraɗiyya a Afirka.
Dimokuraɗiyyar Afirka: Ana zaɓen shugaban ƙasa a Sao Tome and Principe
Shugaba mai ci Carlos Vila Nova na fuskantar abokin hamayya na jam'iyya Nito Viegas D'Abreu, wani ɗanmajalisa mai ci na majalisar dokoki

Masu kaɗa ƙuri’u a tsibirin na Sao Tome and Principe, wadda ake yi wa kallon abin koyi na dimokuraɗiyya a Afirka, suna kaɗa ƙuri’u a zaɓen shugaban ƙasa ranar Lahadi.

Shugaba mai ci Carlos Vila Nova yana fuskantar abokin hamayya na jam’iyya Nito Viegas D'Abreu, wani ɗanmajalisa mai ci da ke da goyon bayan tsohon Firaminista Patrice Trovoada, tare da ‘yantakara biyu masu zaman kansu.

Ƙasar, wadda Portugal ta yi wa mulkin mallaka a yankin tekun Guinea, ƙasa ce ta tsibiri mai mutane 200,000 wadda tarihinta ke cike da yunƙurin juyin mulki ciki har da wani yunƙurin kifar da gwamnati da rundunar sojin ƙasar ta daƙile nan-take a shekarar 2022.

Shugaban ƙasar na da muƙamin da ba shi da iko sosai, inda yake wakilta da kuma shelar dokoki yayin da yawancin ikon gwamnati ke hannun Firaminista.

Vila Nova, mai shekra 66, wanda aka zaɓa a matsayin shugaban ƙasa ne a shekarar 2021 da goyin bayan jam’iyyarsa ta ADI, yana bayyana kansa a matsayin mai tabbatar da "lumanar siyasa ta ƙasar".

Ya fuskanci suka game da korar tsohon firayiminista Trovoada a watan Janirun 2025, wani matakin da aka tabbatar da cewa ya saɓa wa tsarin mulki bayan shekara ɗaya .

Wurin yawon buɗe ido

Trovoada, wanda a yanzu shi ne shugaban ADI kuma yake neman ya sake samun muƙamin firayiminista a zaɓen ‘yanmajalisu a wannan watan Satumban, ya nuna goyon bayansa ga abokin hamayyar Vila Nova, Viegas D'Abreu.

Viegas D'Abreu, mai shekara 43, yana gabatar da kansa a matsayin wani wakilin waɗanda aka haifa bayan ƙasar ta samu ‘yancin kai a shekarar 1975.

Sao Tome and Principe na samun kuɗaɗen shiga ne daga noma musamman samar da koko da kofi da borkono.

Yanayin ƙasar na musamman ya sa masu yawon buɗa ido na zuwa ƙasar, musamman attajirai.

Manyan kamfanonin mai sun karɓi lasisin tonon mai da gas daga bakin tekun ƙasar cikin ‘yan kwanakin nan.

Duk da haka ƙasar na tsibiri ya kasance mai dogaro sosai kan tallafi daga ƙetare, inda da yawa daga cikin mutanenta ke rayuwa cikin talauci.

Rumbun Labarai
Ƙoƙarin kawar da sankarau: Manufar Afirka ta kawar da cutar baki ɗaya nan da 2030
Mutane fiye da 4,000 ne suka kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo - Gwamnati
Kwamitin tattaunawa na Libiya ya cim ma matsaya kan tsarin ɗaukar shugaban hukumar zaɓe
Gargadin shugabannin Afirka kan cin abinci a makare da illolin shan siga da giya
Shugaba Biya na Kamaru ya yi sauye-sauye a shugabancin sojin ƙasar
Ghana ta amince da ɗaurin shekara 20 ga duk wanda ya mayar da gonar koko zuwa wani abu daban
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati
Fitacciyar mawaƙiyar Afirka Ta Kudu ta soke kalankuwarta a Legas bayan an kori baƙi daga ƙasarta
Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa
Adadin 'yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya
Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026
Siyasar Kamaru: Ina Shugaba Paul Biya ya shiga?
Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa
Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar
Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu
Chadi ta sanar da shirin fita daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)
An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati
Ƙarin ma'aikatan jinya sun shiga yajin aiki yayin da cutar Ebola ta kama kusan mutum 3,000
Yara na cikin waɗanda aka kashe a harin jirgi marar matuƙi a wata kasuwar Sudan