| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Hukumar NCDC ta Nijeriya ta tabbatar da samun mutum 318 ɗauke da zazzaɓin Lassa da mutuwar mutum 70
Babban Darakta kuma Shugaban Hukumar NCDC, Dakta Jide Idris, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai a ranar Juma’a.
Hukumar NCDC ta Nijeriya ta tabbatar da samun mutum 318 ɗauke da zazzaɓin Lassa da mutuwar mutum 70
Zazzaɓin lassa na yaɗuwa ne daga kashin ɓera / AA
21 Fabrairu 2026

Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Nijeriya, NCDC, ta tabbatar da samun mutane 318 da suka kamu da zazzaɓin Lassa da kuma mutuwar mutane 70 a fadin ƙasar tun daga farkon shekarar 2026.

Babban Darakta kuma Shugaban Hukumar NCDC, Dakta Jide Idris, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai a ranar Juma’a.

Ya ce an samu Jumullar mutane 1,469 da ake zargi da kamuwa da cutar, lamarin da ya sa adadin waɗanda ke mutuwa daga cutar ya kai kashi 22 cikin 100.

A cewarsa, jihohi biyar waɗanda suka haɗa da Edo, Ondo, Taraba, Bauchi da Ebonyi ne ke ɗauke da kashi 91 cikin 100 na dukkan waɗanda aka tabbatar suna ɗauke da cutar. Haka kuma, ƙananan hukumomi goma ne ke da kashi 68 cikin 100 na kamuwa da cutar.

Domin daƙile ɓarkewar cutar, Idris ya ce NCDC ta tura Rundunar Gaggawa ta Kasa zuwa jihohi takwas da suka bayar da rahoton cutar.

Ya ƙara da cewa hukumar tana aiki tare da gwamnatocin jihohi domin ƙarfafa sa ido da kula da marasa lafiya, da kuma wayar da kan al’umma.

“Kare ma’aikatan lafiya na daga cikin manyan abubuwan da muka fi bai wa muhimmanci,” in ji Dakta Idris, inda ya nuna cewa ma’aikatan lafiya 15 sun kamu da cutar tun daga farkon shekarar nan. Ya ce rashin fahimtar hadari da kuma rashin kyakkyawan tsarin kare kamuwa da cutar a wasu cibiyoyin lafiya na daga cikin dalilan hakan.

NCDC ta bayyana wasu kalubale da ake fuskanta, ciki har da rashin bin diddigin waɗanda suka yi mu’amala da masu cutar yadda ya kamata da jinkirin neman magani da kuma ƙarancin kuɗaɗen da jihohi ke warewa don ayyukan rigakafi, lamarin da ka iya ƙara yawan kamuwa da cutar da mace-mace.

Idris ya jaddada rawar da gwamnatocin jihohi ke takawa wajen gano masu cutar da wuri da isar da saƙonnin gargaɗi ga al’umma, da kuma tsaurara aiwatar da matakan kariya da daƙile yaɗuwar cuta.

Har ila yau, ya yi gargaɗi kan yaɗa labaran ƙarya da jita-jita, kamar rahoton ɓarkewar cutar da ba gaskiya ba da aka yaɗa kwanan nan a sansanin Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC) na Jihar Kwara, wanda ka iya kawo cikas ga ƙoƙarin daƙile cutar.

Idris ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su kula da tsaftar muhalli, su adana abinci yadda ya dace, su dakile beraye, tare da gaggauta neman kulawar likita idan aka ga alamun cutar, domin rage yaduwar cutar Lassa.

 

 

Rumbun Labarai
Nijeriya na neman tallafin IMF da Bankin Duniya don rage tasirin yakin Iran kan tattalin arziki
Me ya sa hare-hare ke karu wa a Nijeriya duk da wanzuwar dakarun Amurka?
Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta soma bincike kan zargin kisan fararen-hula a kasuwar Jilli ta Yobe
ADC ta taya sabbin shugabannin jihohi murna, ta tsayar da ranar 12 ga Mayu don rantsar da su
Gwamnatin Nijeriya ta ba da umarnin soke fasfo ɗin mutanen da suka janye daga kasancewa ’yan ƙasar
Man fetur yana tsada sosai, amma mu gode wa Allah halin da muke ciki ya fi na wasu ƙasashe – Tinubu
An gano gawarwaki 61 bayan harin ta'addanci a jihar Neja ta Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda tare da ƙwace makamai a Jihar Filato
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce an kashe dakarunta a harin da Boko Haram ta kai hedkwatarsu a Borno
‘Gwarazan da ba za a iya mantawa da su ba’, Tinubu na juyayin kisan sojojin Nijeriya a harin Borno
Amurka ta bai wa jami'anta umarnin barin ofishin jakadancinta a Nijeriya saboda rashin tsaro a ƙasar
Aƙalla mutum 60 aka kashe a hare-hare daban-daban a arewa maso yammacin Nijeriya cikin mako guda
Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Nijeriya zai habaka a 2026
An mayar da 'yan Nijeriya 179 gida daga Libya
Babbar kotun Nijeriya ta ɗaure 'yanta'adda biyar
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda biyar, sun kama wanda ake zargi da garkuwa da mutane a Filato
Matatar Dangote ta ƙara man da take turawa ƙasashen Afirka yayin da yaƙin Iran ya katse jigilar mai
An buƙaci Nijeriya ta gyara yadda ake bayar da labaran rikice-rikice
An kama mutum biyar kan harbin bindiga ba bisa ƙa’ida ba da 'ya kashe' yarinya Maiduguri a Nijeriya
Abin da ya sa Kano Pillars ta lallasa Bendel Insurance da ci 4-0 — Koci