Rundunar 'yansanda a Nijeriya ta dakile harin da aka kai wa wani sansaninta a Obajana na jihar Kogi
Hukumomin sun ce ana ci gaba da koƙarin gano waɗanda ake zargi da suka tsare.
Rundunar 'yansanda a jihar Kogi da ke yankin arewa maso tsakiyar Nijeriya ta ce jami’anta sun dakile wani yunkurin kai hari kan wani babban sansanin 'yansanda a jihar da wasu "‘yanta’adda" suka yi, inda aka kama wasu da ake zargi da hannu cikin lamarin.
Kafar watsa labarai na ƙasar NTA ya ruwaito cewa Jami'in Hulda da Jama'a na rundunar 'yansandan Jihar Kogi, William Aya ya tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin.
Ya bayyana harin a matsayin wani mataki na ramuwar gayya da aka gaza cimma wanda ya biyo bayan ayyukan tsaro da aka tsananta a baya bayan nan a faɗin jihar.
"Rundunar 'yansandan Nijeriya ta dakile wani yunkurin kai hari kan sansanin Obajana da wasu da ake zargin ‘yanta’adda ne suka shirya kaiwa, an samu nasarar kama wasu da ake zargi," in ji Mista Aya.
A cewar sanarwar 'yansandan, lamarin ya faru ne ‘yan kwanaki kaɗan bayan wani farmaki da 'yan sanda suka jagoranta a ranar 10 ga Janairu, wanda ya mayar da hankali kan muhimman wurare da ake zargi da kuma maɓoyar 'ya ta'adda da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke amfani da su a jihar Kogi.
Fusata ayyukan kai hare-hare
Mista Aya ya ce, aikin da aka gudanar ya samu taimako da haɗin gwiwa daga sashin rundunar 'yansandan sama ta Nijeriya, wadda ta ba da gudanmawa wajen kaddamar da hare-hare ta sama.
Ya kuma ƙara da cewa nasarar wannan aiki ne ya fusata ayyukan kai hare-haren ta'addanci a yankin.
Mai magana da yawun 'yansandan ya ce waɗanda ake zargin sun yi ƙoƙarin ramawa ta hanyar kai hari kan kadarorin 'yansanda da wuraren aiki a sansanin Obajana amma jami'an da ke bakin aiki sun fatattake su.
"Jami'an 'yansanda da ke bakin aiki sun gudanar da wani farmaki mai cike da tsari, wanda ya kawar tare da rage ƙarfin ‘yanta’adda," in ji shi, ya ƙara da cewa an kama wasu da ake zargi a yayin fafatawar, waɗanda da yawa daga cikinsu suka jikkata sakamakon harɓin bindiga.
Rundunar ta ce ana ci gaba da koƙarin gano waɗanda ake zargi da suka tsare.
Tsaro mai rauni
Yunƙurin kai harin ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma yawan tashe-tashen hankula a sassan jihar Kogi.
Rahotannin kafofin watsa labarai na cikin gida a Nijeriya sun bayyana cewa 'yan sanda da sojoji sun ƙaddamar da hare-haren sama da na ƙasa a yankunan dazuzzuka, inda suka wargaza sansanonin 'yan ta'adda da dama.
Waɗannan hare-haren sun biyo bayan jerin hare-hare da sace-sacen mutane, musamman a yankunan Yagba da Kabba-Bunu na jihar.
A ranar 31 ga watan Disamban 2025, wasu da ake zargin 'yan ta'adda ne sun kai hari kan al'ummar Omi-Ara a ƙaramar hukumar Yagba ta Yamma, inda suka sace mazauna da ba a bayyana adadinsu ba.