| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Rundunar 'yansanda a Nijeriya ta dakile harin da aka kai wa wani sansaninta a Obajana na jihar Kogi
Hukumomin sun ce ana ci gaba da koƙarin gano waɗanda ake zargi da suka tsare.
Rundunar 'yansanda a Nijeriya ta dakile harin da aka kai wa wani sansaninta a Obajana na jihar Kogi
Mai magana da yawun 'yan sandan jihar Kogi ya ce wadanda ake zargin sun yi yunkurin kai hari kan kaɗarorin 'yan sanda. / Reuters
13 Janairu 2026

Rundunar 'yansanda a jihar Kogi da ke yankin arewa maso tsakiyar Nijeriya ta ce jami’anta sun dakile wani yunkurin kai hari kan wani babban sansanin 'yansanda a jihar da wasu "‘yanta’adda" suka yi, inda aka kama wasu da ake zargi da hannu cikin lamarin.

Kafar watsa labarai na ƙasar NTA ya ruwaito cewa Jami'in Hulda da Jama'a na rundunar 'yansandan Jihar Kogi, William Aya ya tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin.

Ya bayyana harin a matsayin wani mataki na ramuwar gayya da aka gaza cimma wanda ya biyo bayan ayyukan tsaro da aka tsananta a baya bayan nan a faɗin jihar.

"Rundunar 'yansandan Nijeriya ta dakile wani yunkurin kai hari kan sansanin Obajana da wasu da ake zargin ‘yanta’adda ne suka shirya kaiwa, an samu nasarar kama wasu da ake zargi," in ji Mista Aya.

A cewar sanarwar 'yansandan, lamarin ya faru ne ‘yan kwanaki kaɗan bayan wani farmaki da 'yan sanda suka jagoranta a ranar 10 ga Janairu, wanda ya mayar da hankali kan muhimman wurare da ake zargi da kuma maɓoyar 'ya ta'adda da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke amfani da su a jihar Kogi.

Fusata ayyukan kai hare-hare

Mista Aya ya ce, aikin da aka gudanar ya samu taimako da haɗin gwiwa daga sashin rundunar 'yansandan sama ta Nijeriya, wadda ta ba da gudanmawa wajen kaddamar da hare-hare ta sama.

Ya kuma ƙara da cewa nasarar wannan aiki ne ya fusata ayyukan kai hare-haren ta'addanci a yankin.

Mai magana da yawun 'yansandan ya ce waɗanda ake zargin sun yi ƙoƙarin ramawa ta hanyar kai hari kan kadarorin 'yansanda da wuraren aiki a sansanin Obajana amma jami'an da ke bakin aiki sun fatattake su.

"Jami'an 'yansanda da ke bakin aiki sun gudanar da wani farmaki mai cike da tsari, wanda ya kawar tare da rage ƙarfin ‘yanta’adda," in ji shi, ya ƙara da cewa an kama wasu da ake zargi a yayin fafatawar, waɗanda da yawa daga cikinsu suka jikkata sakamakon harɓin bindiga.

Rundunar ta ce ana ci gaba da koƙarin gano waɗanda ake zargi da suka tsare.

Tsaro mai rauni

Yunƙurin kai harin ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma yawan tashe-tashen hankula a sassan jihar Kogi.

Rahotannin kafofin watsa labarai na cikin gida a Nijeriya sun bayyana cewa 'yan sanda da sojoji sun ƙaddamar da hare-haren sama da na ƙasa a yankunan dazuzzuka, inda suka wargaza sansanonin 'yan ta'adda da dama.

Waɗannan hare-haren sun biyo bayan jerin hare-hare da sace-sacen mutane, musamman a yankunan Yagba da Kabba-Bunu na jihar.

A ranar 31 ga watan Disamban 2025, wasu da ake zargin 'yan ta'adda ne sun kai hari kan al'ummar Omi-Ara a ƙaramar hukumar Yagba ta Yamma, inda suka sace mazauna da ba a bayyana adadinsu ba.

Rumbun Labarai
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya