| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Ƙungiyar Houthi ta yi barazanar haramta wa Isra'ila jigilar kayayyaki a Bahar Rum gaba ɗaya
Kungiyar Houthi ta Yemen ta yi gargadin tsananta kai hare-haren jiragen ruwa da kuma sabbunta na makamai masu linzami, tana mai danganta matakinta da karuwar rikice-rikice a faɗin Gabas ta Tsakiya.
Ƙungiyar Houthi ta yi barazanar haramta wa Isra'ila jigilar kayayyaki a Bahar Rum gaba ɗaya
Isra'ila ta kuma kai hare-hare a yammacin da tsakiyar Iran, inda aka ruwaito fashewar abubuwa a birane da dama, ciki har da Tehran, Isfahan da Tabriz / TRT Afrika Hausa

Kungiyar Houthi ta Yemen ta fada a ranar Litinin cewa za ta sanya dokar "dakatar da zirga-zirgar jiragen ruwa na Isra'ila gaba daya" a Bahar Rum, tana mai gargadin cewa za a sake kai hari kan jiragen ruwa da ke da alaƙa da Isra'ila saboda tashin hankalin yankin da ke dada karu.

'Kungiyar ta yi barazanar haramta wa Isra'ila jigilar kayayyaki ta Tekun Bahar Rum gaba daya yayin da rikicin yankin ke karuwa’

Kungiyar ta kuma ce ta kai hare-haren makamai masu linzami kan abin da ta bayyana a matsayin wuraren da Isra'ila ke kai hari a yankin Jaffa, tana mai ikirarin cewa hare-haren sun cimma manufofinsu da "yanda yakamata."

Hare-haren da ka iya faɗaɗa rikicin yankin

A cikin sanarwar da ta fitar, kungiyar ta ce an kai hare-haren makamai masu linzami ne a matsayin martani ga hare-haren Isra'ila a Iran, Falasdinu, Lebanon, Iraki, da kuma Yemen, tana mai kari da cewa za ta zafafa kai hare-haren sojinta daidai da abubuwan da ke faruwa a ƙasa.

"Mun tabbatar da cewa za mu mayar da martani mai zafi ga zafafan hare-hare,’’ in ji ƙungiyar, tana mai ƙari da cewa ayyukanta za su dada yawa.

Zuwa yanzu dai Isra'ila ba ta mayar da martani nan take kan sabbin iƙirarin ba. Sai dai da safiyar yau Litinin, an rufe sararin samaniyar Isra'ila na ɗan wani lokaci bayan an kawar da wani makami mai linzami da aka harba daga Yemen, a cewar rahotannin kafofin watsa labarai na Isra'ila.

Hakan dai, ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da faɗaɗa tashe-tashen hankula a yankin, ciki har da sanya shingen makamai masu linzami na Iran a arewacin Isra'ila bayan harin da ta kai a yankunan kudancin Beirut.

Kazalika Isra'ila ta kai hare-hare a yammaci da kuma tsakiyar Iran, inda aka ruwaito fashewar abubuwa a birane da dama, ciki har da Tehran, Isfahan, da Tabriz.

Rumbun Labarai
Iran ta dakatar da tattaunawa da Amurka saboda hare-haren Isra'ila a Lebanon: rahoto
Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka a Kuwait bayan hari kan benen sadarwar Hormozgan
Masar ta yi kira ga kwamitin tsaro na MƊD ta dakatar da faɗaɗa [harin] da Isra'ila ke yi a Lebanon
Iran ta ci gaba da aikin samar da gas a wurarenta uku na South Pars da ke cikin teku
Netanyahu ya kira taron gaggawa bayan Hezbollah ta kai hari na ban mamaki ga sojin Isra'ila
Zaman jiragen sojojin Amurka ya janyo wa filin jirgin saman Ben Gurion na Israila asarar $248M
Dakarun Juyin-Juya-Hali na Iran sun ce sun kai hari sansanin Amurka na sama a Kuwait
Amurka ta kai sabbin hare-hare a wuraren soji a kudancin Iran — rahoto
Rundunar sojin Isra'ila ta yi ikirarin kashe shugaban rundunar sojin Hamas a wani babban hari a Gaza
Musulmai sun yi sallar idin Babbar Sallah a Masallacin Ƙudus a Gabashin Birnin Ƙudus da aka mamaye
Iran ta yi iƙirarin harbo jirgin yaki mara matuƙi na Amurka tare da tilasta wa wasu ja da baya
Sojojin Amurka sun kai hari kan jiragen yaƙi na ruwa da wuraren makamai masu linzami a kudancin Iran
Ƙasashe 10 sun gayyaci jakadun Isra’ila kan bidiyon cin zarafin da Ben-Gvir ya yi wa ayarin Sumud
Hezbollah ta ce ta kai hare-hare 24 kan dakarun mamaya na Isra'ila a kudancin Lebanon cikin sa'a 24
Iran ta yi gargaɗin cewa sabon harin Amurka da Isra'ila zai iya faɗaɗa rikici fiye da yankin
Amurka za ta kawo ƙarshen yaƙi da Iran 'cikin gaggawa', a cewar Trump
Iran ta bayyana cikakkun bayanai na shawarwari 14 ga Amurka da nufin kawo ƙarshen yaƙi
'Lokaci na ƙurewa' Trump ya yi gargaɗi ga Iran yayin da ƙofofin diflomasiyya ke rufewa
Saudiyya ta ce an tare jirage uku marasa matuƙa bayan sun shiga sararin samaniyar ƙasar daga Iraq
Amurka ba ta bayar da wani rangwame mai gamsarwa ba a martaninta ga Iran: Kafofin watsa labaran Iran