| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Nijeriya tana cikin tattaunawa da Amurka bayan barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi kan zargin ana yi wa Kiristoci kisan kare dangi a kasar, kamar yadda Ministan Harkokin Wajen Nijeriya ya ce.
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
A farkon Nuwamba 2025, Shugaban Amurka Donald Trump ya yi zargin cewa 'yan ta'adda suna tsananta wa Kiristoci a Najeriya, zargin da Abuja ta musanta.
17 Nuwamba 2025

Nijeriya na tattaunawa da Amurka bayan barazanar Shugaba Donald Trump na daukar matakin soji kan zargin cewa ana azabtar da Kiristoci a kasar, in ji Ministan Harkokin Wajen Nijeriya AFP a ranar Litinin.

"Abin da muke tattaunawa shi ne yadda za mu yi aiki tare don magance kalubalen tsaro wadanda suka shafi duniya baki daya," in ji Minista Yusuf Tuggar a wata hira a babban birnin tarayya Abuja.

A farkon watan Nuwamba Trump ya ce ya bukaci Hedikwatar Tsaro ta Amurka, Pentagon ta tsara wata yiwuwar shirin kai hari a kasar wadda ta fi yawan jama'a a Afirka, saboda 'yan ta'adda suna "kashe Kiristoci sosai."

Da aka tambaye shi ko yana ganin Washington za ta tura sojoji su kai farmaki, Tuggar ya ce: "A'a, bana tunanin haka."

'Tattaunawar ta samu ci gaba'

"Domin muna ci gaba da tattaunawa, kuma kamar yadda na ce, ana samun ci gaba a tattaunawar. Ta wuce wannan mataki."

Shugaban Amurka ya ce addinin Kiristanci na fuskantar "barazanar kawar da shi" a kasar ta Yammacin Afirka, inda ya yi gargaɗi cewa idan Nijeriya ba ta dakatar da kashe-kashen ba, Amurka za ta kai hari kuma "zai kasance cikin sauri kuma mai tsanani."

Nijeriya, wacce ke da mutane kimanin miliyan 230, an raba ta kusan daidai tsakanin kudu mai rinjaye Kiristoci da arewa inda Musulmai suke da rinjaye.

Ta'addanci a Nijeriya yana shafar Kiristoci da Musulmai duka, ba tare da bambanci ba.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?