| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Gagarumar gobara ta laƙume gidaje 1,000 a ƙauyen da ke kan ruwa, tare da raba dubbai da muhallansu
Kusan gidaje 1,000 daga cikin kimanin 1,200 ne suka lalace sakamakon gobarar da ta tashi a Kampung Bahagia, wani ƙauye da ke kan ruwa a birnin gabar teku na Sandakan.
Gagarumar gobara ta laƙume gidaje 1,000 a ƙauyen da ke kan ruwa, tare da raba dubbai da muhallansu
Gagarumar gobara ta laƙume gidaje 1,000 a ƙauyen da ke kan ruwa, tare da raba dubbai da muhallansu / Reuters

Hukumomi sun kaddamar da aikin ceto da agaji bayan wata gagarumar gobara ta ƙone kauyen da ke kan ruwa a Malaysia, inda ta lalata daruruwan gidaje.

Kusan gidaje 1,000 daga cikin kimanin 1,200 ne suka lalace a gobarar a Kampung Bahagia, wani kauye mai gidaje a kan ruwa a garin bakin teku na Sandakan a ranar Lahadi, in ji hedikwatar labarai ta gwamnati, Bernama.

Fiye da mutum 9,000 suka rasa matsuguni sakamakon gobarar.

An ƙone fili mai fadin fiye da hekta huɗu, kuma yanayin ragin ruwa a teku ya yi wahala wajen samun isasshen ruwa don aikin kashe gobara, a cewar shugaban Cibiyar Wuta da Ceton Sandakan, Jimmy Lagung.

Firaminista Anwar Ibrahim ya ce ya yi mamaki lokacin da ya ji labarin gobarar, kuma gwamnatin tarayya tare da gwamnatin jihar Sabah suna haɗin gwiwa don ba da tallafin kayayyakin buƙata da wuraren zama na wucin gadi ga wadanda abin ya shafa.

Lagung ya ce an tura ɗimbin 'yan kashe gobara zuwa wurin bayan tashar ta karɓi kiran gagagwa game da gobarar da karfe 1.32 na daren Lahadi (1732 GMT a ranar Asabar).

An ayyana wurin a matsayin yankin da bala'i ya shafa da karfe 4 na safe (2000 GMT a ranar Asabar).

An kawo ƙarshen aikin kashe gobara da ƙarfe 12 na ranar Lahadi, ba tare da rasa rai ba.

Walter Kenson, shugaban Kwamitin Kula da Bala'o'in Gundumar Sandakan, ya ce bincike da aka yi a kauyen ya gano cewa gidajen mazauna da abin ya shafa "ba su da aminci na zama a ciki."

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Wani sanatan Amurka ya fada wa Majalisar Dattawa cewa ƙasar ta yi asarar jirage 39 a yakin Iran
Ƙarancin abinci: Toshe Mashigar Hormuz na barazana ga mutum miliyan 45 a duniya in ji MDD
WHO ta ce duniya ba ta fuskantar barazana bayan ɓullar cutar hantavirus a wani babban jirgin ruwa
Jamus ta waiwayi Turai bayan shirin janye sojojin Amurka
Washington ta kashe dala biliyan 25 tun fara yaƙin Amurka da Isra'ila a Iran - Pentagon
UAE ta fita daga Ƙungiyar Ƙasashe Masu Arzikin Fetur ta Duniya, OPEC
Waye zai zama Sakatare Janar na MDD? Macky Sall na fuskantar abokan takara daga Latin Amurka
Abubuwan da muka sani game da harbe-harben da aka yi a taron liyafar Trump da manema labarai
Trump ya ce harbin da aka yi ba zai hana shi samun nasara a yakin Iran ba
An fitar da Trump daga wajen liyafa da 'yanjarida yayin da 'wata kara' ta haifar da fargabar tsaro
'Gigitaccen mahaukaci': Sanatocin Amurka sun caccaki barazanar Trump ga Iran a matsayin laifin yaƙi
Trump: Za a kai wa tashoshin lantarki da gadojin Iran hari idan ba a buɗe Mashigar Hormuz ba
Mai Bai wa Trump Shawara kan Addini tana shan raddi bayan ta kwatanta shi da Yesu Almasihu
Damuwar 'yan Republican na ƙaruwa gabanin zaɓukan rabin wa'adi saboda tasirin yaƙin Iran
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya