| Hausa
TURKIYYA
3 minti karatu
Turkiyya na sanya ido sosai kan rikici a Syria a wani bangare mai muhimmanci kan tsaron kasarta
Majiyoyin tsaron Turkiyya sun shaida wa TRT World cewa Turkiyya tana bibiyar rikicin da ake yi a Syria don kare fararen hula da hana kwararar 'yan gudun hijira saboda yaƙin da ake yi a Aleppo tsakanin sojojin Syria da ƙungiyar ta'addanci ta YPG.
Turkiyya na sanya ido sosai kan rikici a Syria a wani bangare mai muhimmanci kan tsaron kasarta
Yan ta'addan YPG sun kashe a kalla fararen hula takwas kuma sun raba dubban dubatan mutane da muhallansu a yayin sabon tashin hankali a Aleppo. / Reuters
9 Janairu 2026

Tyrkiyya ta ce tana sa idanu sosai kan halin da ake ciki a Siriya, inda aka ba da fifiko ga hadin kan siyasa na ƙasar, da kiyaye iyaka da tsarin gwamnatin ƙasa, kamar yadda bayanan da majiyoyin tsaro na Turkiyya suka shaida wa TRT World.

Hukumar Leƙen Asiri ta Kasa (MIT) tana mai da hankali kan rage tasirin rikice-rikicen yankunan kan iyaka a Turkiyya, tana bibiyar yiwuwar kwararar masu ƙaura daga cikin Siriya, da kuma taimakawa wajen tabbatar da tsaron fararen hula a yankin, in ji majiyoyin.

“Ana nazarin sabbin arangama a Aleppo, musamman a unguwannin Sheikh Maqsoud, Ashrafiyeh da Beni Zaid, inda ake da al’ummar Ƙurdawa da yawa, tsakanin rundunar soja ta Siriya da 'yan YPG,” in ji majiyoyin.

YPG ita ce reshen ƙungiyar ta’addanci ta PKK a Siriya.

Majiyoyin tsaro sun ce rikici ya barke ne bayan YPG ta kasa girmama yarjejeniyar 10 ga watan Maris da gwamnatin Siriya.

Ayyukan ƙungiyar, waɗanda ake ganin suna rushe ƙoƙarin sulhu, sun haifar da tsoro na ƙarin tabarbarewar zaman lafiya a yankin.

’Yan ta’addan YPG sun kashe akalla fararen hula takwas kuma sun tilasta wa dubban mutane yin hijira a cikin sabon tashin hankalin a Aleppo.

Gwamnatin Siriya ta daɗe tana bin hanyar magance rikicin ba tare da tashin hankali ba, kamar yadda majiyoyin tsaron suka jaddada, inda ta yi tayi masu yawa ga YPG tare da ci gaba da buɗe hanyoyin tattaunawa.

“Sai dai, YPG ta yi watsi da waɗannan tayin, sannan ta ɗauki matsayi mai tsauri, tana neman ƙarin lokaci,” in ji majiyoyin.

Kafa iko a yankunan da ake fafatawa

Rundunar soja ta Siriya ta karɓe iko da unguwannin Ashrafiyeh da Beni Zaid bayan fafatawa, in ji majiyoyin, yayin da ayyukan soji ke ci gaba a Sheikh Maqsoud.

Sojojin Siriya sun ayyana dakatar da kai hare-hare a yankunan da ake rikicin a Aleppo, suna bai wa YPG damar janyewa zuwa gabashin Kogin Furat don hana sake barkewar tarzoma.

Amurka da Turkiyya sun yaba da sanarwar tsagaita wutan da Damaskus ta yi, inda suka bayyana ta a matsayin hanyar hana ƙarin zubar da jini da kuma kwararar ‘yan gudun hijira masu yawa.

Ankara ta yi watsi da duk wani yunkuri na ƙungiyar ta’addancin YPG na amfani da fararen hula a matsayin garkuwa a cikin yakin da take yi da rundunar soja ta Siriya.

Turkiyya na ci gaba da neman warware tashin hankalin a Siriya cikin lumana, bisa ga ikon Siriya na ƙasa da martaba iyakokinta, in ji majiyoyin.

Dukkan hukumomi suna faɗake

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan yana bibiyar ci gaban lamuran sosai, yayin da MIT ke ci gaba da tuntuɓar hukumomin Amurka da na Siriya tana isar da saƙonni, a cewar majiyoyin.

Ana kuma sa ido kan abubuwan da suke faruwa sosai tare da Ma’aikatar Harkokin Waje da Ma’aikatar Tsaron Kasa, yayin da ma’aikatan MIT a yankin ke aiki ba dare ba rana, cikin kwanaki 7 a mako, in ji majiyoyin.

Turkiyya ta jaddadawa a koyaushe cewa, ba za a iya raba zaman lafiya da tsaron Siriya da nata ba, tana kira ga duka ɓangarorinsu yi haƙuri su koma tattaunawa.

Majiyoyin tsaro sun jaddada cewa Kurdawan Siriya 'yan ƙasar ne, kuma kare haoƙƙoƙinsu na daga cikin abubuwan da Turkiyya ke fifitawa.

A cewar majiyoyin, babban burin Ankara shi ne samun zaman lafiya mai ɗorewa da kwanciyar hankali a Siriya tare da kiyaye dukkan iyakarta, kuma tana sa ran YPG za ta ɗauki wata hanya da za ta taimaka ga haɗin kan Siriya a siyasance, da zaman lafiya na al'umma, da haɗin kan al’umma a zamantakewa.

Rumbun Labarai
Adadin jama'ar Turkiyya ya kai miliyan 86 a 2025 yayin da jama'ar ƙasar ke ƙara yawa
Matar Shugaban Turkiyya da Sarauniyar Jordan sun ƙara jaddada ƙawance a Istanbul
Turkiyya ta kama jami'an Mossad na Isra'ila biyu a Istanbul kan leƙen asiri
Shugaba Erdogan ya tuna da girgizar ƙasa, ya ce ‘Turkiyya ta cika alkawarinta‘ na sake gina gidaje
Turkiyya ta bunƙasa taimakon da ta ke ba Somaliya na sojojin sama da ƙasa don yaƙi da ta'addanci
Shugaban Turkiyya Erdogan ya gana da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a Riyadh
Shugaban Turkiyya zai ziyarci Saudiyya da Masar a cikin wannan makon
Fidan na Turkiyya ya gargaɗi Amurka kan kai wa Iran hari, ya ce Tehran a shirye take ta tattauna
Zaman lafiyar Iran na da muhimmanci ga tsaron yankin: Turkiyya
Turkiyya da Nijeriya sun ƙudiri aniyar kyautata alaƙar kasuwanci, zuba jari da tsaro
Erdogan da Trump sun tattauna kan Syria da Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza
Turkiyya ta goyi bayan Nijeriya a yaƙi da ta'addanci yayin da Erdogan ya karbi baƙuncin Tinubu
Ziyarar Tinubu a Turkiyya: Muhimman abubuwa a tsarin dangatakar Nijeriya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwaransa na Nijeriya Tuggar
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya da takwaransa na Nijeriya za su gana kan cinikayya da tsaro
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hidan ya yaba da "Kwamitin Zaman Lafiya" na Gaza
Turkiyya ta ɗauki dukkan yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da mahimmanci: Erdogan
Fidan na Turkiyya zai halarci bikin sa hannu na 'Hukumar Zaman Lafiya' ta Gaza a Switzerland
An tono makarantar Islamiyya mai shekara 900 yayin aikin sabunta birni a yankin Anatolia a Turkiyya
‘Syria ta ‘yan Syria ce’: Erdogan ya yaba da yarjejeniyar zaman lafiya ta Damascus