Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yanke ƙauna kan yiwuwar sake tattaunawa da Amurka bayan abin da ya bayyana a matsayin wani lamari "mai tsabar muni."
Da yake magana a wata hira da kafar watsa labarai ta PBS News ranar Litinin, Araghchi ya yi tsokaci kan ko sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, zai buɗe ƙofar sabuwar tattauna ko kuma tsagaita wuta.
Ya ce zai "yi sauri da yawa a yi wani tsokaci” kan lamarin.
"Amma ba na tunanin maganar sake tattaunawa da Amurkawa ko yarjejeniya da Amurkawa za ta kasance a cikin ajandarmu bayan Amurkawa sun aikata mummunan lamari," in ji Araghchi .
Ya yi ishara ga yaƙin kwanaki 12 da aka yi a watan Yunin da ya gabata a lokacin da Isra’ila da dakarun Amurka suka kai hari kan tashoshin nukiliyar Iran yayin da ake tattaunawa tsakanin Tehran da Washington .
Da yake magana game da zagaye na baya bayan nan na tattaunawa a Geneva a ƙarshen watan Fabrairu, Araghchi ya ce ɓangarorin biyu sun bayyana tattaunawar a matsayin mai alamar alfanu a tsarin shiga-tsakani na ƙasar Oman.
"Amma kuma, bayan zagaye uku na tattaunawa, kuma bayan tawagar Amurka a tattaunawar ta bayyana da kanta cewa mun samu gagarumin ci-gaba, duk da haka, sun yanke shawarar kai mana hari," in ji shi.
"Saboda haka ba na tunanin sake tattaunawa da Amurkawa zai kasance a cikin ajandarmu."
Tashe-tashen hankula na yanki
Da yake magana game da katse harkoki a kasuwancin man duniya, Araghchi ya ce ba Iran ba ce ta janyo koma-baya ga yadda ake samar da man fetur da kuma jigilarsa a duniya.
"Wannan ba laifinmu ba ne. Wannan ba tsarinmu ba ne," in ji shi.
Ya ce hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai ne suke janyo tsaikon.
Araghchi ya ce waɗannan hare-haren sun sa yankin na ƙara zama maras zaman lafiya kuma mara tsaro.
"Wannan shi ya sa tankoki da jiragen ruwan suke tsoron wucewa ta mashigin ruwan Hormuz," in ji shi.
Araghchi ya yi watsi da zarge-zargen cewa Iran tana katse jigilar mai da gangan ta hanyar kai hare-hare kan jiragen ruwa da ke safarar makamashi a yankin.
"Muna fuskantar wani mataki na tsangwama, wanda kwata-kwata bai dace da doka ba, kuma abin da muke yi shi ne matakin kare kai, wanda ya dace da doka," in ji shi.
Ya ƙara da cewa Tehran ta gargaɗi ƙasashen yankin cewa idan Amurka ta kai hari kan Iran kai-tsaye, Iran za ta mayar da martani ta hanyar kai hare-hare kan sansanonin Amurka da kayayyakinta a faɗin yankin.
"Kuma sakamakon hakan, yaƙin zai bazu zuwa dukkan yankin," in ji Araghchi.
"Ba mu muke da alhaƙin wannan ba."
















