| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Iran ta harba makamai masu linzami Isra'ila, 9 sun mutu a Beit Shemesh, 12 sun mutu a faɗin ƙasar
Harin ya taɓa gidajen ƙarƙashin ƙasa na kariya daga bam yayin da jerin makamai masu linzami suka keta tsarin tsaron sararin samaniyar Isra'ila, inda suka kashe 12 tare da jikkata kimanin mutum 60.
Iran ta harba makamai masu linzami Isra'ila, 9 sun mutu a Beit Shemesh, 12 sun mutu a faɗin ƙasar
Hoton jirgi mara matauƙi na yadda hare-haren Iran ya yi da Beit Shemesh a Isra'ila / Reuters / Reuters
2 Maris 2026

Iran ta zafafa hare-haren makamai masu linzaminta kan Isra’ila bayan hare-haren haɗin gwiwa da Isra’ila da Amurka suka kai mata inda suka kashe jagoran addinin ƙasar Ali Khamenei.

Waɗanda suka mutu a Isra’ila sakamakon hare-haren Iran sun kai aƙalla mutum 12 inda fiye da mutum 50 suka jikkata, in ji rahotanni daga majiyoyin Isra’ila.

Tsare-tsaren sararin samaniyar Isra’ila masu matakai, ciki har da Iron Dome da David's Sling da Arrow, sun kakkaɓo da yawa daga cikin makamai masu linzamin da ke shiga ƙasar, amma wasu da suka faɗo kai-tsaye sun janyo jikkata fararen hula.

Hari ɗaya tilo da ya fi muni ya faru ne ranar Lahadi a Beit Shemesh, wani birni da ke yammacin birnin Ƙudus, inda wani makami mai linzamin Iran ya faɗa kai-tsaye kan wata unguwa.

Makamin ya lalata gidaje da dama, ciki har da wani gida na ƙarƙashin ƙasa da aka gina a matsayin kariya daga harin bam, lamarin da ya sa saman gidan ya faɗi.

Magen David Adom (MDA), hukumar ba da agajin gaggawa ta Isra’ila, ta fara ba da rahoton yadda adadin mace-mace ke ƙaruwa a ranar, daga shida zuwa takwas, sannan zuwa mutum tara da aka kashe — inda gommai suka jikkata, kuma aƙalla biyu daga cikin su suna cikin matsanancin hali.

Kafar Times of Israel ta ba da rahoton cewa adadin waɗanda aka kashe a Beit Shemesh ya kai tara, inda ta bayyana yanayin a matsayin mai cike da ruɗani kuma gidaje da maɓoyar da aka yi don kauce wa harin bam suka lalace sosai.

Masu AlakaTRT Afrika - Iraniyawa suna zanga-zanga bayan Amurka da Isra'ila sun kashe Khamenei

Kazalika jaridar Jerusalem Post ta bayyana cewa ‘yan Isra’ila tara ne aka kashe a harin, inda aka ba da rahoton ƙarin jikkata da kuma rasa rayuka yayin da gine-gine suka rufta.

Daga farko daga daren Asabar zuwa ranar 1 ga watan Maris, wasu jerin hare-haren makamai masu linzami sun sauka a Tel Aviv, inda suka kashe mata biyu — ɗaya daga cikinsu mai shekara 32 inda ɗaya kuma take da shekara 68 wadda ta mutu yayin da take tserewa zuwa maɓoya — da kuma jikkata fiye da mutum 120 , in ji MDA da sauran rahotanni.

Kafafen watsa labara na Haaretz da The Times of Israel sun ba da rahoton ƙarin hare-hare da suka janyo rauni a birnin Ƙudus da kuma sauran wuraren da ke kusa da su, ciki har da rauni na tarkacen ƙarafuna inda aƙalla mutum bakwai suka jikkata a Birnin Ƙudus.

Hukumar da ke tabbatar da cewa Isra’ilawa suna cikin shiri a lokacin rikici ko bala’i ta yi kira ga mazauna ƙasar su mayar da hankali inda ƙararrawar gargaɗi da ke ta kaɗawa a faɗin yankunan tsakiya da na arewacin Isra’ila.

Rumbun Labarai
Iran ta ce Amurka ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta
Iran na iya janyewa daga yarjejeniyar tsagaita wuta idan Isra'ila ta cigaba da yaƙar Lebanon: Rahoto
Sharuɗɗa 10 na zaman lafiya da Amurka ta amince da su a yarjejeniyar tsagaita wuta da Iran
Mazauna Tehran sun fada halin rashin tabbas bayan barazanar Trump ta baya bayan nan
Abubuwan da ya kamata mu sani game da daftarin yarjejeniyar Amurka da Iran
Masar ta haɗa kai da Turkiyya da Pakistan don shiga tsakanin Iran da Amurka – Kafafen  Yaɗa Labarai
Amurka da Iran na duba yiwuwar cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 45: Rahoto
Amurka ta ceto direban jirgin F-15 na biyu da ake nema a Iran — Trump
Tururin nukiliya zai jawo asarar rayuka a manyan biranen ƙasashen Gulf ba Tehran ba: Araghchi
Farashin kayan abinci, man fetur da takin zamani ya ƙaru saboda yaƙin Gabas ta Tsakiya: MDD
Yadda yakin Gabas ta Tsakiya zai shafi ƙasashen Afirka a gajeren lokaci, in ji wani rahoto
Iran ta harbo jirgin yaƙin Amurka samfurin F-35
Makamai masu linzami na Iran na jarraba ƙarfin garkuwar makamai masu linzami a sararin samaniya
Iran ta ce Mashigar Teku ta Hormuz a bude take ga duniya, amma a rufe ga maƙiya
Iran ta yi ruwan makamai masu linzami kan Isra’ila bayan Trump ya yi iƙirarin daƙile ƙarfin sojinta
Isra’ila ce ummul aba'isin haramtaccen yaƙi da Iran: In ji Erdogan na Turkiyya
Kalin ya karɓi baƙuncin tawagar Hamas don tattauna shirin zaman lafiya na Gaza
Trump ya ce Amurka za ta bar Iran cikin makonni 2 zuwa 3
Iran ta ce lokaci ya yi da Saudiyya za ta kori sojojin Amurka daga yankinta
Yadda yaƙin Iran zai iya rikita kasuwancin duniya ta Mashigar Teku ta Bab al Mandeb