Iran ta harba makamai masu linzami Isra'ila, 9 sun mutu a Beit Shemesh, 12 sun mutu a faɗin ƙasar

Harin ya taɓa gidajen ƙarƙashin ƙasa na kariya daga bam yayin da jerin makamai masu linzami suka keta tsarin tsaron sararin samaniyar Isra'ila, inda suka kashe 12 tare da jikkata kimanin mutum 60.

By
Hoton jirgi mara matauƙi na yadda hare-haren Iran ya yi da Beit Shemesh a Isra'ila / Reuters / Reuters

Iran ta zafafa hare-haren makamai masu linzaminta kan Isra’ila bayan hare-haren haɗin gwiwa da Isra’ila da Amurka suka kai mata inda suka kashe jagoran addinin ƙasar Ali Khamenei.

Waɗanda suka mutu a Isra’ila sakamakon hare-haren Iran sun kai aƙalla mutum 12 inda fiye da mutum 50 suka jikkata, in ji rahotanni daga majiyoyin Isra’ila.

Tsare-tsaren sararin samaniyar Isra’ila masu matakai, ciki har da Iron Dome da David's Sling da Arrow, sun kakkaɓo da yawa daga cikin makamai masu linzamin da ke shiga ƙasar, amma wasu da suka faɗo kai-tsaye sun janyo jikkata fararen hula.

Hari ɗaya tilo da ya fi muni ya faru ne ranar Lahadi a Beit Shemesh, wani birni da ke yammacin birnin Ƙudus, inda wani makami mai linzamin Iran ya faɗa kai-tsaye kan wata unguwa.

Makamin ya lalata gidaje da dama, ciki har da wani gida na ƙarƙashin ƙasa da aka gina a matsayin kariya daga harin bam, lamarin da ya sa saman gidan ya faɗi.

Magen David Adom (MDA), hukumar ba da agajin gaggawa ta Isra’ila, ta fara ba da rahoton yadda adadin mace-mace ke ƙaruwa a ranar, daga shida zuwa takwas, sannan zuwa mutum tara da aka kashe — inda gommai suka jikkata, kuma aƙalla biyu daga cikin su suna cikin matsanancin hali.

Kafar Times of Israel ta ba da rahoton cewa adadin waɗanda aka kashe a Beit Shemesh ya kai tara, inda ta bayyana yanayin a matsayin mai cike da ruɗani kuma gidaje da maɓoyar da aka yi don kauce wa harin bam suka lalace sosai.

Kazalika jaridar Jerusalem Post ta bayyana cewa ‘yan Isra’ila tara ne aka kashe a harin, inda aka ba da rahoton ƙarin jikkata da kuma rasa rayuka yayin da gine-gine suka rufta.

Daga farko daga daren Asabar zuwa ranar 1 ga watan Maris, wasu jerin hare-haren makamai masu linzami sun sauka a Tel Aviv, inda suka kashe mata biyu — ɗaya daga cikinsu mai shekara 32 inda ɗaya kuma take da shekara 68 wadda ta mutu yayin da take tserewa zuwa maɓoya — da kuma jikkata fiye da mutum 120 , in ji MDA da sauran rahotanni.

Kafafen watsa labara na Haaretz da The Times of Israel sun ba da rahoton ƙarin hare-hare da suka janyo rauni a birnin Ƙudus da kuma sauran wuraren da ke kusa da su, ciki har da rauni na tarkacen ƙarafuna inda aƙalla mutum bakwai suka jikkata a Birnin Ƙudus.

Hukumar da ke tabbatar da cewa Isra’ilawa suna cikin shiri a lokacin rikici ko bala’i ta yi kira ga mazauna ƙasar su mayar da hankali inda ƙararrawar gargaɗi da ke ta kaɗawa a faɗin yankunan tsakiya da na arewacin Isra’ila.