| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Amurka ta ƙulla yarjejeniya da Nijeriya don mayar da hankali kan kyautata kiwon lafiyar Kiristoci
A watan jiya, Trump ya ce Amurka ta shirya kai hari a Nijeriya domin kawar da masu yi wa "Kiristoci kisan gilla."
Amurka ta ƙulla yarjejeniya da Nijeriya don mayar da hankali kan kyautata kiwon lafiyar Kiristoci
Abuja ta ce ba ta lamunta da tsanantar addini ko kaɗan ba. / Others
21 Disamba 2025

Amurka ta sanar da cewa ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya don ƙarfafa tsarin kiwon lafiya na Nijeriya, 'yan makonni bayan Shugaba Donald Trump ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.

A ƙarƙashin yarjejeniya ta shekaru biyar, Washington za ta bayar da kusan dala biliyan 2.1 don taimakawa wajen hana yaɗuwar HIV, tarin fuka, zazzaɓin cizon sauro da cutar polio, da kuma kare lafiyar mata masu juna biyu da yara, in ji wani mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka a ranar Asabar.

Nijeriya ta yi alƙawarin kashe ƙarin kusan dala biliyan 3 a cikin shekaru biyar masu zuwa, in ji kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka, yana mai ƙarawa da cewa yarjejeniyar ta ƙunshi "mayar da hankali kan tallafa wa cibiyoyin kiwon lafiya masu alaƙa da addinin Kiristanci."

A watan jiya, Trump ya ce Amurka ta shirya kai hari a Nijeriya domin kawar da mutanen da ya ce suna yi wa "Kiristoci kisan gilla."

Shugaban Amurka ya ce Kiristanci na fuskantar "barazana ta gushewa" daga Nijeriya da "ƙasashe da dama," yana mai cewa gwamnatinsa ba za ta bari a ci gaba da tsangwamar Kiristoci ba.

Masu AlakaTRT Afrika - Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla

Washington ta sanya Nijeriya a cikin jerin ƙasashe da ake "sanya wa idanu sosai" dangane da 'yancin addini kuma ta taƙaita bayar da biza ga 'yan Nijeriya.

An ƙulla wannan yarjejeniyar ce "bayan gwamnatin Nijeriya ta yi wasu gyare-gyare domin bayar da fifiko ga kare Kiristoci daga tashin hankali," in ji mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen.

Mahukuntan Nijeriya sun sha bayyana cewa ba a nuna tsangwama ga mabiya kowane addini.

Nijeriya ta daɗe tana fama da rikice-rikice na ƙabilanci da addini da kuma na ƙungiyoyin da ke iƙirarin jihadi, kuma rikicin ya halaka aƙalla mutane 40,000, ciki har da Kiristoci da Musulmai, tare da tilasta wa kusan mutane miliyan biyu yin gudun hijira, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

A farkon watan Disamba, Amurka ta sanya hannu kan yarjejeniyar tallafin kayan kiwon lafiya ta dala biliyan 2.5 da Kenya - wannan ita ce yarjejeniya ta biyu tun bayan da Trump ya soke hukumar USAID da ke tallafa wa ƙasashen duniya musamman kan harkokin lafiya.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Amurka ta ƙaƙaba wa wasu 'yan Nijeriya takunkumi kan zargin ta'addanci da laifuka ta intanet
Bikin kamun kifi na Argungu: Kifin da ya kai kilogiram 59 ya ɗau hankalin dubban mutane
Sojojin Amurka sun isa arewa maso gabashin Nijeriya
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku