Dakarun Nijeriya sun kashe aƙalla 25 daga cikin ‘yan ƙungiyar ISWAP mai alaƙa Daesh a wani samame da suka kai a jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar, kamar yadda hukumomi suka bayyana.
Sani Uba, jami’in watsa labaran runduna ta musamman da ke yankin, ya bayyana ranar Lahadi cewa dakarun sun kai samamen kan ‘yan ISWAP ne a Limankara da Kukawa, kamar yadda wata sanarwa da ya fitar ta bayyana.
“Yayin musayar wutar, an kashe ‘yanta’adda 15 sannan gomman ‘yanta’adda sun tsere da raunuka na harbi,” in ji Uba.
Ya ƙara da cewa na’urar tattara bayanai ta sama ta bi ‘yanta’adda da ke tserewa kan babura biyar, inda wani harin ba tare da kuskure ba “ya kashe ƙarin ‘yanta’adda 10 ".
Ya ƙara da cewa an lalata ababe da yawa na tsaro da na jigila da ‘yanta’addan ke amfani da su.
An kuma ƙwace motoci biyu da makamai da kuma harsasai masu yawa daga hannun ƙungiyar.
Nijeriya ta daɗe tana fama da hare-hare daga ‘yanbindiga da kuma ƙungiyoyin ‘yanta’adda na Boko Haram da ISWAP a sassan ƙasar.
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi iƙirarin cewa ana yi wa Kiristoci “kisan gilla” a Nijeriya.
Amma mahukunta a Abuja da yawancin ƙwararru sun ce tashin hankalin da ake yi a Nijeriya na shafar Kiristoci da Musulmai ne ba tare da wariya ba.
Ranar 25 ga watan Disamba, sojin Amurka sun ƙaddamar da hare-haren sama a jihar Sokoton Nijeriya.
Hukumomin Nijeriya daga baya sun bayyana cewa an ɗauki matakin ne tare da saninsu kuma an kai hari ne kan ‘yanta’adda masu alaƙa da Daesh.
An tura wasu sojojin Amurka 100 zuwa Nijeriya a wani ɓangare na ƙarin haɗin kai na soji domin yaƙar ‘yanta’adda. Sai dai kuma Nijeriya ta ce dakarun Amurka ba za su shiga yaƙi ba kai-tsaye.













