| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Nijeriya ta fara kwashe 'yan ƙasarta daga Iran
Abike Dabiri ta bayyana cewa jami'an Nijeriya suna jira a kan iyaka domin karɓar 'yan ƙasar da ke tserewa daga yaƙin Iran, tana mai ƙarawa da cewa kawo yanzu babu ɗan Nijeriya da ya mutu a yaƙin.
Gwamnatin Nijeriya ta fara kwashe 'yan ƙasarta daga Iran
Abike Dabiri-Erewa, shugabar hukumar da ke kula da 'yan Nijeriya da ke ƙetare / User Upload
8 awanni baya

Gwamnatin Nijeriya ta fara kwashe ‘yan ƙasarta daga Iran, inda jami’ai ke musu rakiya daga kan iyakar Armenia yayin da yaƙin Amurka da Isra’ila kan Tehran ke ci gaba da ƙamari.

Shugabar hukumar da ke kula da ‘yan Nijeriya da ke ƙasashen waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X ranar Talata, ta ce ana raka ‘yan ƙasar da ke son barin ƙasar Iran ta hanyar kan iyaka.

Ta kuma bayyana cewa jami’an Nijeriya suna jira a kan iyaka domin tarbar ‘yan ƙasar da ke tserewa daga yaƙin Iran, tana mai ƙarawa da cewa ba a samu wani ɗan Nijeriya da ya mutu a yaƙin ba.

“Jami’an ofishin jakadancin Nijeriya a Iran suna raka duk wani ɗan ƙasar da ke son tafiya gida zuwa kan iyakar Armenia domin samun damar wucewa cikin aminci.

Masu AlakaTRT Afrika - Rikicin Gabas ta Tsakiya ya tilasta wa jiragen ruwa na duniya sauya hanya suna bi ta Afirka

“Babu wani ɗan Nijeriya a Iran da yaƙin ya shafa amma jami’anmu suna kan iyaka domin tarbar duk wanda ke son tafiya,” in ji ta.

Ba ta ba da haƙiƙanin adadin ‘yan Nijeriya da ke Iran ba ko kuma adadin waɗanda aka riga aka kwashe.

Matakin na kuɓutar da ‘yan Nijeriyar na zuwa ne kwanaki 11 da fara yaƙin da ya kashe mutum fiye da 1,300, tare da jikkata da kuma raba wasu mutane da gidajensu.

Ma’aikatar lafiyar Iran ta ce hare-haren Amurka da Isra’ila sun kashe fiye da mutum 1,300 a Iran, inda fiye da mutum 12,000 suka jikkata.

Iran ta ce mata 200 na cikin waɗanda aka kashe, ciki har da yara mata ‘yan makarantar Minab 168.

Kazalika, kimanin ma’aikatan jinya 55 sun jikkata yayin da aka kashe 11 daga cikinsu.