| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Amurka ta ƙaƙaba wa wasu 'yan Nijeriya takunkumi kan zargin ta'addanci da laifuka ta intanet
Daga cikin waɗanda aka ƙaƙaba wa takunkumin kuma aka ƙwace kadarorinsu sakamakon alaƙa da ƙungiyoyin 'yanbindiga su ne manyan waɗanda ke da alaƙa da Boko Haram da ISWAP da kuma Ansaru.
Amurka ta ƙaƙaba wa wasu 'yan Nijeriya takunkumi kan zargin ta'addanci da laifuka ta intanet
Wasu daga cikin 'yan Nijeriya da gwamnatin Trump ta sanya wa takunkumi suna da alaƙa da Boko Haram da ISWAP da kuma Ansaru. / AP
17 Fabrairu 2026

Gwamnatin Amurka ta ƙaƙaba takunkumai kan wasu ‘yan Nijeriya 18 da wasu ƙungiyoyi kan zargin ta’addanci da laifuka ta intanet da safarar miyagun ƙwayoyi.

Wannan na zuwa ne yayin da Washington ke ƙarfafa haɗin kai na soji da Nijeriya domin daƙile barazanar masu tsattsauran ra’ayi.

A ƙarƙashin shirye-shiryen da ofishin Amurka da ke kula da kadarori na ƙetare (OFAC), an ayyana ɗaiɗaikun mutane da ƙungiyoyi a wani mataki na musamman mai nuna aikata ta’addanci a duniya (SDGT) da jerin barazana masu alaƙa da intanet (CYBER2) da kuma safarar ƙwayoyi (SDNTK).

Boko Haram da ƙungiyoyi masu alaƙa da IS

A cikin waɗanda aka ƙaƙaba wa takunkumi kuma aka ƙwace kadarorinsu sakamakon alaƙa da ƙungiyoyin ‘yanbindiga akwai manyan waɗanda ke da alaƙa da Boko Haram da ISWAP da Ansaru — ƙungiyoyin da suka shafe fiye da shekara goma suna kai hare-hare a arewa maso gabashin Nijeriya.

Cikin waɗanda aka sanya sunayensu a jerin sunayen ‘yanta’adda na duniya akwai tsohon shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau da kwamandoji masu alaƙa da ISIS Abu Musab al-Barnawi da Khalid al-Barnawi, tare da wasu masu hulɗa da su da ke da alaƙa da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

Masu AlakaTRT Afrika - Sojojin Amurka sun isa arewa maso gabashin Nijeriya

Har wa yau akwai Salih Yusuf Adamu da Ibrahim Ali Alhassan da Surajo Abu Bakr Muhammad da Abdurrahman Ado Musa da Ali Abbas Usman Jega.

Kazalika an ƙaƙaba wa reshen Nijeriya na ƙungiyar RIHS mai rajin farfaɗo da Islama domin zargin taimaka wa ayyukan masu tsattsauran ra’ayi.

Takunkumai masu alaƙa da laifukan intanet da safarar ƙayoyi

A wani mataki na daban, an bayyana sunayen wasu ‘yan Nijeriya biyar — wani da ake ce wa Nnamdi Orson Benson da Abiola Ayorinde Kayode da Alex Afolabi Ogunshakin da Micheal Olorunyomi da kuma Richard Izuchukwu Uzuh — a ƙarƙashin dokar hana laifukan intanet ta Amurka US CYBER2 bisa rawar da ake zargin sun taka a wajen shirya manyan damfara ta intanet.

Mutane biyu, wani mai suna Wole A. Ogungbuyi da Babestan Oluwole Ademulero, kuwa an ayyana su a matsayin gaggan masu safarar miyagun ƙwayoyi kan zargin da aka yi musu na kasancewa cikin masu safarar miyagun ƙwayoyi a ƙasashen duniya.

Rumbun Labarai
Bikin kamun kifi na Argungu: Kifin da ya kai kilogiram 59 ya ɗau hankalin dubban mutane
Sojojin Amurka sun isa arewa maso gabashin Nijeriya
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka