| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
'Yanbindiga sun raba fiye da mutum 300,00 da gidajensu a jihar Neja – Gwamna Bago
Waɗannan hare-haren sun katse hanyoyin samun mutane tare da tilasta wa mutane barin gidajensu da kuma ƙarfafa rashin tsaro a yankunan karkara.
'Yanbindiga sun raba fiye da mutum 300,00 da gidajensu a jihar Neja – Gwamna Bago
Gwamnan Jihar Niger Mohammed Umar Bago
2 Maris 2026

Gwamnan Jihar Neja a arewacin Nijeriya, Umaru Mohammed Bago, ya bayyana cewa fiye da mutum 300,000 ne hare-haren ‘yanbindiga babu ƙaƙƙautawa suka raba da gidajensu a ƙananan hukumomi 10 na jihar.

Jihar Neja tana ɗaya daga cikin jihohin da hare-haren ‘yanbindiga suka fi ƙamari inda ƙungiyoyin ‘yanbindiga suke yawan kai hare-hare kan al’umomi masu rauni kuma suke kashe tare da garkuwa da mazauna wuraren ciki har da ‘yan makaranta.

Waɗannan hare-haren sun katse hanyoyin samun mutane da tilasta wa mutane barin gidajensu da kuma ƙarfafa rashin tsaro a yankunan karkara.

Saboda haka, iyalai da yawa a halin yanzu suna rayuwa ne cikin tsoro na dindindin. Mutane sun bar gonaki saboda tsoron tashin hankali yayin da iyaye suke jin tsoron tura ‘ya’yansu makaranta.

Hare-haren babu ƙaƙƙautawa ba harkar noma kawai suka shafa ba, sun dagula harkar jinƙai a jihar.

Masu AlakaTRT Afrika - Gwamnatin Jihar Neja ta karɓi ɗalibai 100 na St. Mary’s Catholic School da aka ceto

Da yake magana da ‘yanjarida ranar Asabar a Minna, babbin birnin jihar bayan ya karɓi tallafin jinƙai daga gwamnatin tarayya, Gwamna Bago ya bayyana cewa ana ƙoƙarin tattara cikakkun bayanai game da mutanen da aka raba da muhallansu saboda ana ci gaba da kai hare-hare kan ƙananan hukumomi.

“A halin yanzu, ƙiyasi kawai za mu iya bayarwa. Aƙalla muna da mutane fiye da 300,000 da aka kora daga digajensu a ƙananan hukumomi fiye da 10 da ke fama da rashin tsaro,” in ji shi.

Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa tana aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya cikin al’ummonin da ke fama da rashin tsaro.

Ya bayyana fatansa cewa matakan tsaron da ake ɗauka za su sa waɗanda aka raba da muhllansu su koma gida da kuma koma rayuwa yadda suka saba.

Rumbun Labarai
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda tare da ƙwace makamai a Jihar Filato
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce an kashe dakarunta a harin da Boko Haram ta kai hedkwatarsu a Borno
‘Gwarazan da ba za a iya mantawa da su ba’, Tinubu na juyayin kisan sojojin Nijeriya a harin Borno
Amurka ta bai wa jami'anta umarnin barin ofishin jakadancinta a Nijeriya saboda rashin tsaro a ƙasar
Aƙalla mutum 60 aka kashe a hare-hare daban-daban a arewa maso yammacin Nijeriya cikin mako guda
Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Nijeriya zai habaka a 2026
An mayar da 'yan Nijeriya 179 gida daga Libya
Babbar kotun Nijeriya ta ɗaure 'yanta'adda biyar
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda biyar, sun kama wanda ake zargi da garkuwa da mutane a Filato
Matatar Dangote ta ƙara man da take turawa ƙasashen Afirka yayin da yaƙin Iran ya katse jigilar mai
An buƙaci Nijeriya ta gyara yadda ake bayar da labaran rikice-rikice
An kama mutum biyar kan harbin bindiga ba bisa ƙa’ida ba da 'ya kashe' yarinya Maiduguri a Nijeriya
Abin da ya sa Kano Pillars ta lallasa Bendel Insurance da ci 4-0 — Koci
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda yaran Ado Aleiro
‘Yanta’adda sun kai hari ofishin ‘yansanda a Borno, sun kashe jami’ai huɗu
Rundunar Sojin Nijeriya ta amince a tura ƙarin sojoji 850 zuwa Filato saboda matsalar tsaro
Dalilin da ya sa Shugaba Tinubu ya gana da waɗanda harin Filato ya shafa a filin jirgin sama
A karon farko Nijeriya ta fitar da ganga 950,000 ta ɗanyen mai samfurin Cawthorne zuwa Indiya
Jam'iyyar ADC ta zargi gwamnatin Nijeriya kan matakin INEC na cire David Mark daga shugabancinta
Nijeriya za ta bayar da ƙarin ɗanyen mai ga matatar man Dangote a watan Mayu