Rundunar ‘yansandan jihar Kebbi ta tabbatar da cewa an kashe mutum 33 a wani harin da aka kai gundumar Bui a ƙaramar hukumar Arewa bayan an yi wani fashin shanu da makami.
Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan jihar Kebbi, Bashir Usman ne ye bayyana wannan a wata sanarwa.
“A matsayin martani, rundunar tare da sojoji da sauran hukumomin tsaro, ta tura ƙarin ma’aikata da kayayyakin aiki zuwa wuraren da lamarin ya faru. A halin yanzu ana ci gaba da sintiri na tabbatar da iko a wurin domin tabbatar da zaman lafiya,” in ji sanarwar Usman.
Hukumomin ‘yansanda sun bayyana matuƙar rashin jin daɗinsu game da rasa rayukan kuma sun miƙa saƙon ta’aziyya ga al’ummar ƙaramar hukumar Arewa Community.
Sanarwar ta ƙara da cewa bincike na farko-farko ya nuna cewa wasu da ake ganin mayaƙan Lakurawa ne suka shiga gundumar Bui domin fashin shanu.
An yi imanin cewa maharan sun tsallako wurin ne daga ƙaramar hukumar Gudu a jihar Sokoto mai maƙwabtaka.
Labari mai alaƙa: Mutane da dama sun rasa rayukansu a hare-haren Lakurawa a Jihar Kebbi a Nijeriya
Rahotanni sun ce mazauna wurare kamar Mamunu da Awasaka da Tungan Tsoho da Makangara da Kanzo da Gorun Naidal da kuma Dan Mai Ago sun haɗa kai domin tunkarar maharar lamarin da ya kai ga rangama na makamai da ƙungiyar ‘yan bindigar.
Rundunar ‘yansandan jihar ta jaddada cewa duk abinda ya shafi ƙungiyoyin masu aikata laifuka na buƙatar tsara matakin tsaro na hadin gwiwa.
Hukumomi sun yi kira ga mazanuna wuraren su ba da rahoton duk wani abin da ba su yarda da shi ba ta hnayoyin sadarwa na tsaro maimakon tunkararsu kai tsaye, suna masu gargadin cewa irin wannan arangamar na da matuƙar haɗari.












