Iran ta ce Amurka ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta
“Rushe madogarar da za a iya dogara da ita don yin sulhui” kan tsagaita buɗe wuta tsakanin Iran da Amurka ta riga ta rushe, wanda hakan ya sa ci gaba da tattaunawar ya zama “abin da ba zai yiwu ba,” a cewar Mohammad Bagher Ghalibaf.
Shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya bayyana cewa hare-haren da ake ci gaba da kaiwa Lebanon, kutsen da jirage marasa matuƙa suka yi a sararin samaniyar Iran, da kuma ƙin amincewa Iran ta samar da sinadarin uranium, sun kawo babban ƙalubalen ga ci gaba da tattaunawar da ake yi.
Ghalibaf ya bayyana a shafinsa na X cewa “manufar da za a iya dogara da ita don yin sulhu” kan tsagaita wuta tsakanin Iran da Amurka ta riga ta rushe, abin da ya sa ci gaba da tattaunawar ya zama “abin da ba zai yiwu ba.”
Ya nuna cewa wannan keta yarjejeniya yana ƙara dagula batun tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, wanda ke nuna damuwar Iran game da bin sharuɗɗan tsagaita wuta.
Ghalibaf ya lissafa abubuwa uku da ya ce Amurka ta saɓa a cikin shirin tsagaita wutar: ci gaba da kai hare-hare a Lebanon, shigar jirgi maras matuƙa sararin samaniyar Iran, da kuma hana ƙasar haƙƙinta na tace sinadarin nukiliya.
Hakan na zuwa ne yayin da yarjejeniyar tsagaita wuta mai rauni tsakanin Iran da Amurka ta shiga rana ta biyu a ranar Alhamis, a daidai lokacin da Isra’ila ta ƙaddamar da ruwan bama-bamai a Lebanon.
Amurka da Iran duka sun yi ikirarin samun nasara bayan sun amince da tsagaita wuta ta mako biyu da tattaunawa da nufin kawo ƙarshen yaƙin da ya kashe dubban mutane a faɗin Gabas ta Tsakiya kuma ya haifar da matsalar tattalin arziki a duniya.
Sai dai rarrabuwar kawuna a yarjejeniyar ta fito fili a ranar Laraba yayin da Isra’ila ta kai mafi girman hare-harenta a maƙwabciyarta Lebanon, har da tsakiyar birnin Beirut da ke cike da mutane.
Adadin waɗanda suka mutu sakamakon hare-haren Isra’ila a faɗin Lebanon ya karu zuwa 254, yayin da 1,165 suka ji rauni, kamar yadda Hukumar Kare Muradin Jama’a ta Lebanon ta bayyana, wanda hakan ya nuna ɗaya daga cikin ranaku mafiya muni.
Isra’ila ta ce hare-haren da take kaiwa a Lebanon ba sa cikin yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta tsakanin Amurka da Iran da aka cimma a daren ranar Talata, matakin da Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ya goyi baya, kwanaki kaɗan kafin ya jagoranci tattaunawa da Iran a Pakistan.
Lokaci na “Babban Fatan”
Bayan raunin da yarjejeniyar take da shi, wadda aka cimma sa’o’i kaɗan kafin cikar wa’adin da Shugaban Amurka Donald Trump ya ɗiba, wani babban jami’in Amurka ya ce shirin Iran na maki 10 ba sharuɗɗa ɗaya ne da fadar White House ta amince da su ba don dakatar da yaƙin.
A Lebanon, inda babban jami’in kare haƙƙin ɗan’Adam na MDD Volker Turk ya bayyana yawan kisan da ake yi a matsayin “mai ban tsoro,” hare-haren da aka kai a babban birnin ƙasar, Beirut, ba tare da gargaɗi ba sun haifar da tsoro da fargaba.
Rundunar dakarun juyin juya halin Musulunci ta Iran ta yi gargaɗin cewa za su “sauke nauyin da ke kansu kuma su mayar da martani” idan Isra’ila ba ta daina hare-haren ba.
Wadannan maganganu sun zo ne kafin tattaunawa mai muhimmanci da ake sa ran yi a Pakistan ranar Juma’a.
Rahotanni sun nuna cewa an sake rufe hanyar ruwa ta “Strait of Hormuz” duk da yarjejeniyar tsagaita buɗe wutar, abin da fadar White House ta kira “sam ba za a amince da shi ba.”
Iran ta sanar da wasu hanyoyin daban na jiragen ruwa da ke ratsa ta mashigar Hormuz a ranar Alhamis, tana mai bayyana barazanar nakiya a babban yankin da ke kewaye da kasarta.
Firaiministan Pakistan, Shehbaz Sharif, wanda ƙasarsa ta shiga tsakani wajen cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta, ya buƙaci dukkan ɓangarorin da su “yi haƙuri kuma su mutunta yarjejeniyar tsagaita buɗe wutar har tsawon makonni biyu” domin ba wa diflomasiyya dama.
A birnin Tehran, tituna sun kasance shiru fiye da yadda aka saba a ranar Laraba, inda shaguna da dama suka kasance a rufe bayan dogon dare na fargaba ga mazauna garin da ke tsoron gagarumin harin Amurka.
“Kowa yana cikin kwanciyar hankali yanzu,” in ji Sakineh Mohammadi, wata mata mai shekaru 50, inda ta ƙara da cewa tana “alfahari” da ƙasarta.
“Muna cikin nutsuwa yanzu.”
A ranar Laraba, shugabannin ƙasashe da dama na Turai, Canada da Burtaniya sun ce dole ne a tattauna “kawo ƙarshen yaƙin cikin sauri kuma hakan ya zama na dindindin,” yayin da Fafaroma Leo ya yaba da wannan lokaci a matsayin lokaci na “fatan gaske.”