Kafar watsa labaran gwamnatin Iran ta ce an kashe Jagoran Addinin ƙasar Ayatollah Ali Khamenei a harin da Isra'ila da Amurka suka kai, lamarin da ya sanya kiraye-kiraye ga rundunar juyin-juya-hali ta Revolutionary Guards domin ta ɗauki matakin ramuwar gayya.
Gidan talbijin na ƙasar Iran ranar Lahadi ya sanar da makokin kwana 40 tare da bayar da hutun kwana bakwai bayan kisan shugaban addinin ƙasar mai shekara 86, wanda ke kan mulki tun shekarar 1989.
Kafofin watsa labaran Iran sun ruwaito cewa an kashe ‘yar Ayatollah Ali Khamenei da jikarsa da kuma surukinsa a harin.
"Shahadar da shugaban addini ya yi ba za ta sa a manta da tafarkinsa da jagorancinsa ba, hasali ma, za a tabbatar da su ne bisa ƙarfin gwiwa da jajircewa," a cewar mai gabatar da labarai a gidan talbijin na gwamnatin Iran.
Rundunar juyin-juya-hali ta Revolutionary Guards ta sha alwashin yin ramuwar gayya kan “wadanda suka kashe” Khamenei.
"Rayuwar gayya da ƙasar Iran za ta yi zai kasance mai tsanani kuma cike da karsashi, sannan waɗanda suka kashe Shugaban Al’umma ba za su ci bulus ba," in ji wata sanarwa da Rundunar juyin-juya-hali ta fitar.
An kashe jagoran addinin Iran lokacin da yake taro da na hannun damansa
Harin da Isra’ila da Amurka suka kai Iran ranar Asabar ya zo ne a lokacin da Khamenei yake gudanar da taro da manyan masu ba shi shawara, a cewar wsu majiyoyi na gwamnatin Amurka.
Isra’ila ta yi iƙirarin cewa an kashe Khamenei ne tare da manyan na hannun damansa da suka haɗa da Ali Shamkhani, tsohon sakataren Majalisar Tsaron Ƙasa, da Mohammad Pakpour, kwamandan Rundunar juyin-juya-hali ta Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC).













