Abin da Daso ta fada wa TRT Hausa kafin rasuwarta

Abin da Daso ta fada wa TRT Hausa kafin rasuwarta

A yau ne ake cika kwana shida da rasuwar fitacciyar tauraruwar Kannywood Saratu Gidado (Daso) wadda ta rasu ranar Talata a birnin Kano da ke Nijeriya. Marigayiyar ta taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan jama'a ta hanyar finafinanta. Sai dai baya ga harkar fim, Daso ta yi fice wajen tallafa wa marasa galihu da marayu, kamar yadda ta shaida mana a wata hira da muka yi da ita ranar 9 ga watan Fabrairun 2024.