Gwamnatin Nijeriya ta gargaɗi masu sakin-baki kan tsaro
Ministan watsa labaran ƙasar Mohammed Idris ya ce a shirye suke su karɓi shawarwari kan yadda za a inganta tsaro a ƙasar, amma ba za su bari wasu manyan mutane kamar malamai da ƴan siyasa su jefa Nijeriya cikin ruɗani ba.