| hausa
AFIRKA
3 minti karatu
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Dan Gaddafi ya yi niyya ya bar Lebanon zuwa wani wuri na "sirri", a cewar lauyansa, yana mai cewa yana da fasfo din Libya.
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Dan Gaddafi ya yi niyya ya bar Lebanon zuwa wani wuri na "sirri", a cewar lauyansa, yana mai cewa yana da fasfo din Libya.
11 Nuwamba 2025

Lebanon ta saki Hannibal Gaddafi, ɗan tsohon shugaban Libya Muammar Gaddafi, bisa sharadin beli, bayan da ya shafe kusan shekaru goma yana ɗaure a kurkuku, in ji lauyansa.

"Mun bar wurin, yanzu ya samu yanci," in ji Laurent Bayon a ranar Litinin, awanni kaɗan bayan an biya kudin beli har dala 900,000.

Ana zargin Hannibal Gaddafi mai shekaru 49 da boye bayanai game da bacewar limamin Shi’a na Lebanon Mussa Sadr a Libya a 1978, amma ba a taba gurfanar da shi a kotu ba.

A lokacin batan Sadr, Hannibal yana da shekaru biyu.

"An biya jinginar ne da safiyar yau," in ji Lauya Bayon kamar yadda ya fada tun da fari a ranar Litinin. "A karshe Hannibal Gaddafi zai sami yanci. Wannan shi ne ƙarshen wani mafarki mai muni da ya ɗauki shekaru 10 a rayuwarsa."

A watan Oktoba, wani alkalin kotu ya umurci a saki Gaddafi idan an biya jinginar dala miliyan 11, wanda aka rage zuwa $900,000 makon da ya gabata bayan ƙorafin tawagar kare shari'a.

Wata majiya a bangaren shari'a a Lebanon ta tabbatar a ranar Litinin cewa an biya jinginar, kuma tawagar lauyoyinsa na kammala tsare-tsaren sakin sa.

Bayon ya ce wanda yake karewa zai bar Lebanon zuwa wani wuri 'na sirri', ya kuma ce yana da fasfo na Libya.

"An tsare Gaddafi ba tare da dalili ba a Lebanon har tsawon shekaru 10 ne saboda tsarin shari'ar kasar bai kasance mai 'yanci ba," in ji Bayon.

Ya ce sakin wanda yake karewar na nuna dawo da 'yancin shari'a ƙarƙashin gwamnati mai kawo sauyi ta Lebanon da aka kafa a watan Janairu.

Mussa Sadr — wanda ya kafa ƙungiyar Amal, wacce yanzu ta kasance abokiyar haɗin gwiwa ta Hezbollah — ya ɓata yayin ziyarar hukuma a Libya, tare da wani mai taimaka masa da kuma wani ɗan jarida.

Beirut ta dora laifin bacewar tasu a kan shugaba na Libya a lokacin, Muammar Gaddafi, wanda aka kawar da shi kuma aka kashe shi bayan gomman shekeru a tashin hankalin da aka yi a kasar a 2011.

Dangantaka tsakanin kasashen biyu ta yi sanyi tun bayan bacewar wadannan mutane uku.

Hannibal, wanda ya auri Aline Skaf, wata mai tallan ayan kawa daga Lebanon, ya tsere zuwa Siriya bayan barkewar tashin hankali a 2011 a Libya.

An sace shi a Disamban 2015 inda wasu maza masu makamai suka kai shi Lebanon, inda hukumomi suka kwato shi daga hannun masu garkuwa sannan daga baya suka tsare shi.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD