| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Obasanjo ya musanta neman wa’adi na uku, ya ce da ya ga dama da ya samu
“Ni ba wawa ba ne. Da a ce ina son wa’adi na uku, na san yadda zan yi na nema. Kuma babu wani ɗan Nijeriya, mai rai ko matacce, da zai ce na kira shi na gaya masa ina son wa’adi na uku,” in ji tsohon shugaban ƙasar.
Obasanjo ya musanta neman wa’adi na uku, ya ce da ya ga dama da ya samu
Obasanjo ya mulki Nijeriya daga 1976 zuwa 1979, sannan ya sake mulkarta daga 1999 zuwa 2007
21 Satumba 2025

Tsohon Shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya karyata zargin da aka jima ana yi masa kan cewa ya taɓa neman tsawaita wa’adin mulkinsa, inda ya jaddada cewa bai taɓa neman wa’adi na uku ba.

Ya bayyana haka ne a yayin wani taro na Democracy Dialogue da Gidauniyar Goodluck Jonathan ta shirya a Accra, Ghana.

Obasanjon ya ce babu wani ɗan Nijeriya, mai rai ko matacce, da zai iya cewa gaskata cewa ya taɓa roƙon goyon baya domin neman wa’adi na uku.

“Ni ba wawa ba ne. Da a ce ina son wa’adi na uku, na san yadda zan yi na nema. Kuma babu wani ɗan Nijeriya, mai rai ko matacce, da zai ce na kira shi na gaya masa ina son wa’adi na uku,” in ji tsohon shugaban ƙasar.

Obasanjo ya jaddada cewa a zamanin mulkinsa ya nuna ƙwarewarsa wajen cim ma manufofin ƙasa da ke da wuyar cimmawa, inda ya kawo misalin yadda Nijeriya ta samu afuwar bashi a lokacin mulkinsa a matsayin babban ƙalubale fiye da neman wa’adi na uku.

“Na kan faɗa musu cewa idan na iya samun afuwar bashi, wanda ya fi wahalar samu fiye da wa’adi na uku, to da ina so na samu wa’adi na uku, da na samu shi ma,” in ji shi.

Ya kuma gargaɗi shugabanni masu zama a kujerar mulki fiye da wa’adinsu, inda ya jaddada cewa imani da cewa mutum ba za a iya rayuwa ba sai da shi “laifi ne a wurin ubangiji.”

Olusegun Obasanjo, wanda tsohon soja ne ya fara mulkar Nijeriya daga shekarar 1976 inda ya miƙa mulki ga gwamnati farar hula a 1979.
Daga baya ya dawo a matsayin shugaban ƙasa da aka zaɓa ta hanyar dimokuraɗiyya daga 1999 zuwa 2007, bayan sojoji sun sake miƙia mulki ga farar hula.

Obasanjo ya taka muhimmiyar rawa wajen gyaran tattalin arziki, sauye-sauyen siyasa, da kuma ƙarfafa matsayi da mutuncin Nijeriya a harkokin ƙasa da ƙasa.

Rumbun Labarai
Rundunar sojin Nijeriya ta kuɓutar da masu yi wa ƙasa hidima 47 daga 'yan Boko Haram a Borno
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 15% kan shigar da fetur da dizal cikin ƙasar
'Musulmai ne Boko Haram ta fara yi wa ɓarna': AU ta yi watsi da Trump kan kisan kiyashi a Nijeriya
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya