| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Fiye da kashi 35 na yaran Nijeriya na fama da rashin abinci mai gina jiki – NARD
A wani rubutu da ta wallafa a X a ranar Alhamis, NARD ta ce fiye da kashi 35 cikin 100 na ‘yan ƙasa da shekara biyar suna fama da matsalar.
Fiye da kashi 35 na yaran Nijeriya na fama da rashin abinci mai gina jiki – NARD
Yaran Nijeriya fiye da kasi 35% na fama da rashin abinci mai gina jiki – NARD
2 Oktoba 2025

Ƙungiyar Likitocin Masu Aikin Neman Ƙwarewa ta Ƙasa (NARD) ta bayyana cewa fiye da kashi 35 cikin 100 na yara ‘yan Nijeriya da ke ƙasa da shekaru biyar na fama da rashin abinci mai gina jiki, inda ta bayyana matsalar a matsayin babban ƙalubale ga lafiyar jama’a.

A wani rubutu da ta wallafa a X a ranar Alhamis, NARD ta ce fiye da kashi 35 cikin 100 na ‘yan ƙasa da shekara biyar suna fama da matsalar.

“Rashin abinci mai gina jiki yana da babban tasiri wajen mutuwar yara. Haka kuma yana shafar ci gaban ƙwaƙwalwa, saurin kamuwa da cututtuka, da kuma aikin ƙasa,” in ji ƙungiyar.

NARD ta bayyana cewa matakan magance matsalar sun haɗa da rabon abinci na musamman da ake amfani da shi wajen magance matsalar rashin abinci mai gina jiki (RUTF), da shirin al’umma na kula da rashin abinci (CMAM), da kuma ba da shawara kan ciyar da jarirai da ƙananan yara (IYCF).

Bincike ya nuna waɗannan dabaru suna taimakawa sosai wajen ƙara yawan murmurewa da kuma samun lafiyar yara, in ji ƙungiyar.

“Mambobin NARD na gaba-gaba wajen aiwatar da shirye-shiryen yaki da rashin abinci mai gina jiki da kuma bincike a faɗin Nijeriya,” in ji ƙungiyar.

Ƙungiyar ta yi kira da a ba da tallafi ga shirye-shiryen abinci masu ɗorewa domin kare lafiyar yara a faɗin ƙasa.

A watan Agusta, Gwamnatin Tarayya ta bayyana matsalar rashin abinci mai gina jiki a Nijeriya a matsayin “matsalar gaggawa ya ƙasa”.

Asarar da ake samu a duk shekara saboda rashin abinci mai gina jiki ta haura dala biliyan 1.5, in ji mai taimaka wa shugaban ƙasa kan lafiyar jama’a, Uju Rochas-Anwuka.

Rochas-Anwuka ya bayyana cewa wannan matsala tana rage ƙarfin ɗan adam da kuma ci gaban ƙasa.

A farkon watan Yuli, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya gargadi cewa rashin abinci mai gina jiki yana hana kusan kashi 40 cikin 100 na yara ‘yan ƙasa da shekaru biyar ci gaban da ya kamata su samu.

A yayin taron ƙasa kan Abinci da Tsaron Abinci a Abuja, ya bayyana wannan matsala a matsayin “ƙalubalen ƙasa.”

Ya kuma jaddada cewa wannan tunatarwa ce kan cewa rashin wadatar abinci ba yunwa kaɗai ba ne.

Rumbun Labarai
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso