| Hausa
AFIRKA
1 minti karatu
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar
Dakarun gabashin Libya sun ce an kashe sojoji uku yayin da aka kama wasu a wani harin da aka kai wurin ƙetare kan iyaka na Al-Toum tsakanin Libya da Nijar.
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar
Rundunar sojin gabashin Libya ta yi imanin cewa 'yan daba masu aikata laifuka da ke fasaƙurin kayayyaki sun far ma sojojinta kana suka tsere Nijar. / Reuters
20 awanni baya

An kashe sojoji uku yayin da wasu suka jikkata a wani harin da ’yanbindiga suka kai kudancin Libya kusa da kan iyakarta da Nijar, kamar yadda rundunar sojin gabashin ƙasar ta bayyana.

A wata sanarwa, rundunar sojin ta ce, an kuma kama sojoji a harin da aka kai wajen ƙetare kan iyaka na Al-Toum.

Ta ce ‘yanbindiga sun kuma far ma Wadi Bougrara da Salvador kusa da kan iyaka da Nijar.

Masu AlakaTRT Afrika - Nijar: Ƙungiyar Daesh ta ɗauki nauyin harin da aka kai sansanin sojin sama na Yamai

Sanarwar ta ce ‘yanbindiga masu aikata laifuka da ke fasa-ƙaurin kayayyaki’ ne suka kai harin, tana mai ƙarawa da cewa “an samu an sake tsare” wuraren da aka kai harin inda dakarun tsaro suka bazama wuraren domin farautar maharan “waɗanda bisa ga dukkan alamu sun tsere ta Nijar.”

Daga farko wata ƙungiyar ‘yanbindiga da ke kiran kanta “‘Yan juyin-juya-hali na Kudu” ta yi iƙirarin cewa ta karɓe iko da wurin ƙetare kan iyaka na Al-Toum tsakanin Libya da Nijar.