| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
Da dakarun operation Hadin Kai suka sami labarin, sai suka yi ta kan ‘yan ta’addan a inda suke a hanyar Mangari  inda mayaƙan suka tsere a gigice.
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
Sojojin sun ƙona gidajen wucin-gadin da suka samu a sansanin 'yan ta'addan / Nigerian army

Rundunar Operation Hadi Kai da ke yaƙi da ‘yan ta’addan Boko Haram a arewa maso gabashin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da aka yi garkuwa da su tare da daƙile harin ‘yan Boko Haram.

A wata sanarwar da ta fitar ranar Lahadi, rundunar ta ce lamarin ya auku ne ranar 9 ga watan Nuwamba a Jihar Borno bayan dakarun sun samu labarin cewa mayaƙan Boko Haram suna kama mutane da motaci a kan hanyar Buratai zuwa Kamuye.

Da dakarun operation Hadin Kai suka samu labarin, sai suka yi ta kan ‘yan ta’addan a inda suke a hanyar Mangari  inda mayaƙan suka tsere a gigice.

“Binciken da aka yi a yankin ya gano matsugunan wucin-gadi na ‘yan ta’adda sannan an kuɓutar da mutum 86 da aka yi garkuwa da su ciki har da maza da mata da ƙananan yara,” in ji sanarwar da Sani Uba, mai magana da yawun rundunar Operation Hadin Kai ya sanya wa hannu.

“Ababen da aka ƙwace sun haɗa da bindiga ƙirar AK-47 ɗaya da gidajen harsasai biyar da harsasai 73 da jidiga huɗu da motocin fararen-hula biyar da babura biyar da kuma babur mai ƙafa uku guda biyu,” in ji sanarwa.

Kazalika sanarwa ta ce sojojin sun lalata sansanin ‘yan ta’addan.

A wani labarin makamancin haka kuma, sanarwar ta ce sojojin da aka tura Mangada sun kama mutum 29 da ke taimaka wa ‘yan ta’adda da abubuwan amfanin yau da kullum a kan hanyarsu ta zuwa Chilaria da wasu kayayyaki.

 “Kayayyakin da aka ƙwace a hannunsu sun haɗa da a-kori-kura biyu da babur mai ƙafa uku ɗaya da ke ɗauke da man fetur da ya kai kimanin lita 1,000a cikin jarka  da galan huɗu  na baƙin mai da sabbin tayoyin motar mai bindiga da tarin magunguna da kuma abinci mai yawa,” a cewar sanarwar.

Ta ƙara da cewa an kammala ayyukan ba tare da wani soja ya ji ciwo ba, lamarin da ya sa manyan sojoji suka yaba da irin bajintar da sojojin Operation Hadin Kai suke nunawa a arewa maso gabashin Nijeriya.

Rumbun Labarai
Sojojin Nijeriya sun kashe Abu Khalid Al Muhajir da wasu  kwamandojin ISWAP tara a Borno
Masarautar Kano ta musanta bidiyon da ake yadawa kan Sarki Sanusi II ya samu 'carry-over' a jami'a
Super Falcons da Indomitable Lionesses na gogayyar shiga Gasar Kofin Duniya
Gwamnatin Nijeriya za ta fara sarrafa kayayyakin tsara iyali a cikin ƙasar
Hukumar EFCC ta rufe asusun gwamnatin Jihar Osun kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamna
Rundunar sojin Nijeriya ta sanya tukuicin N60m kan kwamandan ISWAP da mataimakinsa
An yi motsin ƙasa a wasu sassan Abuja
An saki gomman mutanen da aka yi garkuwa da su a Jihar Kwara bayan wata shida a hannun ‘yanta'adda
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin 'yanta'adda na garkuwa  da mutane 31 a Borno
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Nijeriya ta lalata makamai guda 2,819 da ta kama a matakin dakile rashin tsaro
'Yansandan InterPol sun tasa ƙeyar ɗan China daga Nijeriya kan safarar namun daji