| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
Da dakarun operation Hadin Kai suka sami labarin, sai suka yi ta kan ‘yan ta’addan a inda suke a hanyar Mangari  inda mayaƙan suka tsere a gigice.
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
Sojojin sun ƙona gidajen wucin-gadin da suka samu a sansanin 'yan ta'addan
10 Nuwamba 2025

Rundunar Operation Hadi Kai da ke yaƙi da ‘yan ta’addan Boko Haram a arewa maso gabashin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da aka yi garkuwa da su tare da daƙile harin ‘yan Boko Haram.

A wata sanarwar da ta fitar ranar Lahadi, rundunar ta ce lamarin ya auku ne ranar 9 ga watan Nuwamba a Jihar Borno bayan dakarun sun samu labarin cewa mayaƙan Boko Haram suna kama mutane da motaci a kan hanyar Buratai zuwa Kamuye.

Da dakarun operation Hadin Kai suka samu labarin, sai suka yi ta kan ‘yan ta’addan a inda suke a hanyar Mangari  inda mayaƙan suka tsere a gigice.

“Binciken da aka yi a yankin ya gano matsugunan wucin-gadi na ‘yan ta’adda sannan an kuɓutar da mutum 86 da aka yi garkuwa da su ciki har da maza da mata da ƙananan yara,” in ji sanarwar da Sani Uba, mai magana da yawun rundunar Operation Hadin Kai ya sanya wa hannu.

“Ababen da aka ƙwace sun haɗa da bindiga ƙirar AK-47 ɗaya da gidajen harsasai biyar da harsasai 73 da jidiga huɗu da motocin fararen-hula biyar da babura biyar da kuma babur mai ƙafa uku guda biyu,” in ji sanarwa.

Kazalika sanarwa ta ce sojojin sun lalata sansanin ‘yan ta’addan.

A wani labarin makamancin haka kuma, sanarwar ta ce sojojin da aka tura Mangada sun kama mutum 29 da ke taimaka wa ‘yan ta’adda da abubuwan amfanin yau da kullum a kan hanyarsu ta zuwa Chilaria da wasu kayayyaki.

 “Kayayyakin da aka ƙwace a hannunsu sun haɗa da a-kori-kura biyu da babur mai ƙafa uku ɗaya da ke ɗauke da man fetur da ya kai kimanin lita 1,000a cikin jarka  da galan huɗu  na baƙin mai da sabbin tayoyin motar mai bindiga da tarin magunguna da kuma abinci mai yawa,” a cewar sanarwar.

Ta ƙara da cewa an kammala ayyukan ba tare da wani soja ya ji ciwo ba, lamarin da ya sa manyan sojoji suka yaba da irin bajintar da sojojin Operation Hadin Kai suke nunawa a arewa maso gabashin Nijeriya.

Rumbun Labarai
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka