| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP, sun lalata motocin ƙunar-baƙin-wake na 'yan ta'adda
'Yan ta’addan sun yi yunkurin kutsawa cikin sansanin soji na Mairari ta hanyar amfani da motocin ƙunar-baƙin-wake guda biyu. Sai dai sojojin da ke aikin sa ido sun gano tare da tarwatsa motocin kafin su kai ga shiga sansanin.
Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP, sun lalata motocin ƙunar-baƙin-wake na 'yan ta'adda
A yayin wannan aiki, an gano karin gawawwakin ’yan ta’adda tare da kwato makamai, alburusai da kayan aiki da suka bari yayin tserewarsu. / Nigerian army
14 Disamba 2025

Sojojin Operation HADIN KAI (OPHK) sun yi nasarar dakile wani hari da ’yan ta’addar ISWAP suka kai kan sansanin soji a Mairari, lamarin da ya ƙara karya lagon ‘yan ta’addan da ke aikata laifuka a yankin.  

Harin ya fara ne a daren 12 ga Disamban 2025, ya kuma ci gaba zuwa safiyar 13 ga Disamba, inda sojoji suka mayar da martani cikin gaggawa ta hanyar hadin gwiwar dakarun ƙasa da na sama.

A yayin harin, ’yan ta’addan sun yi yunkurin kutsawa cikin sansanin ta hanyar amfani da motocin ƙunar-baƙin-wake guda biyu. Sai dai sojojin da ke aikin sa ido sun gano tare da tarwatsa motocin kafin su kai ga shiga sansanin.

Bidiyon CCTV da bayanan da aka samu daga filin daga sun tabbatar da cewa an kashe ’yan ta’adda da dama, yayin da wasu kuma suka samu munanan raunuka. Waɗanda suka tsira sun tsere suna kwashe gawawwaki da wadanda suka jikkata.

Bayan daƙile harin da ‘yan ta’addan suka yi yunƙurin kaiwa, sojojin OPHK na  tare da taimakon wasu dakaru na musamman waɗanda suka haɗa da ‘yan sanda da ‘yan bijilanti sun gudanar da bincike mai zurfi a yankin.

A yayin wannan aiki, an gano karin gawawwakin ’yan ta’adda tare da kwato makamai, alburusai da kayan aiki da suka bari yayin tserewarsu.

Abubuwan da aka kwato sun hada da bindigogin AK-47, jigidar alburusai, harsasan PKT, gurneti, babura, na’urorin sadarwa, kayan yaki, kayan jinya da sauran kayayyakin da ke nuna ci gaba da ayyukan ta’addanci.

Motocin bama-bamai guda biyu da aka dakile an tarwatsa su ta hanyar wutar kare kai ta sojoji, lamarin da ya haifar da lalacewa a wurare biyu a kan hanya. Muhimmin abu shi ne babu wata nasara da aka samu wajen kutsawa cikin sansanin, abin da ke nuna shirin ko-ta-kwana, sa ido da jajircewar sojoji.

 

 

Rumbun Labarai
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya
Jami’an tsaron Nijeriya sun kwance wani bam da ‘yan ta’adda suka dasa a Zamfara
Nijeriya ta ƙaddamar da tsarin tattalin arzikin halal domin bunƙasa arzikin ƙasar