| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
Nijeriya da Amurka da Birtaniya suna aikin bincike a kan koken ɗin da kuɗinta ya kai dala miliyan 235 da aka kama a tashar jiragen ruwa ta Legas.
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
NDLEA ta gayyaci takwarorinta daga Amurka da Birtaniya domin taimaka wajen gano inda koken ɗin ya fito
12 Nuwamba 2025

Hukumar da ke yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya (NDLEA) ta ce tana aiki da takwarorinta na Amurka da Birtaniya domin bincike kan asalin hodar ibilis da kimarta ta kai dala miliyan 235 da aka kama a tashar jiragen ruwa ta Tincan a Legas, ɗaya daga cikin kame mafi girma da aka yi a tarihin ƙasar.

Hukumar NDLEA ta bayyana a wata sanarwa ranar Talata cewa an gano kilogiram 1,000 na koken ɗin ne a cikin wata kwantena a wajen lodi da sauke kaya na tashar a ƙarshen mako.

Ma’aikatan tashar jiragen ruwan ne suka sanar da NDLEA da sauran jami’an tsaron tashar jiragen ruwan game da abin da ke faruwa.

Bayan an miƙa ƙwayoyin ga hukumar NDLEA ranar Talata, gwaje-gwaje sun tabbatar da cewa hodar koken ce.

Hukumomin da ke yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi na Amurka da na Birtaniya sun shiga cikin masu binciken bisa gayyatar gwamnatin Nijeriya.

"Maƙasudin haɗin kai da abokan aikinmu na ƙasa da ƙasa  shi ne tabbatar da cewa ba a bar wata dama ba... saboda mu iya kama da kuma hukunta duk waɗanda suka kitsa aika wannan a duk inda suke a duniya," kamar yadda Reuters ta ambato shugaban NDLEA, Buba Marwa, yana cewa.

Rumbun Labarai
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka