| hausa
TURKIYYA
3 MINTI KARATU
Turkiyya ta ceto Cibiyar Tarihi ta Srebrenica daga zama dandalin shara
Daraktan cibiyar Tarihi ta Srebrenica ya yaba da kokarin Turkiyya na farfadowa tare da gyara tsarin gine-gine na cibiyar karkashin hukumar Hadin Kai da Ayyuka ta Turkiyya (TIKA).
Turkiyya ta ceto Cibiyar Tarihi ta Srebrenica daga zama dandalin shara
An ware Gidan Tarihi na Srebrenica-Potocari da makabarta da aka binne wadanda aka kashe a 1995 a yankin Potocari na Srebrenica. / Hoto: AA
19 Yuli 2023

Cibiyar Tahiri ta Srebrenica ta kusan cika da "karafa da suka yi tsatsa" idan ba don gudunmawar da Turkiyya ta kai mata ba, in ji daraktanta.

"Ina so na sanar da jama'a abin da Turkiyya ta yi wa cibiyar tarihi ta Srebrenica. Idan ba don Turkiyya da gwamnatin kasar ba, da karafa masu tsatsa ne za su cika ko ina a cikin cibiyar," a cewar Sarki Suljagic, wanda ya tattara tarihin baka daga wadanda suka tsira daga kisan kare-dangi da aka yi a garin Srebrenica na Bosnia da Herzegovina mai cike da tarihi ga gidan talabijin na Hayat TV da ke Bosnia.

“Ba mu da rufi, ba mu da katanga, komai ya ruguje. Hukumar Hadin Kan Turkiyya (TIKA) ta kawo mana mafita. Abin alfahari ne yin aiki tare da abokanmu da ’yan’uwanmu daga Turkiyya,'' in ji shi.

Gidan tarihi na ‘Srebrenica-Potocari Memorial’ da makabarta da aka binne wadanda aka yi wa kisan kare-dangi na 1995 na yankin Potocari na Srebrenica ne.

An ware wajen ne don karrama wadanda aka yi wa kisan kare-dangi na Srebrenica a shekarar 1995, inda ran ‘yan Bosnia Musulmai maza manya da kanana yara sama da 8,000 suka salwanta a garin.

Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana yankin a matsayin wuri da ake “ tsare shi”.

Kisan kare dangi na Srebrenica

Dubban Musulmai maza da yara kanana ne aka kashe bayan harin da dakarun Serb suka kai "yankin da ke da tsaro" na Majalisar Dinkin Duniya a Srebrenica a watan Yulin 1995, duk da kasancewar sojojin Holland da ke aiki a matsayin dakarun kiyaye zaman lafiya na kasa da kasa a wajen.

Dakarun Sabiya sun yi wa Srebrenica kawanya, a kokarin da suka yi wajen kwace yankin daga hannun Musulmai ‘yan Bosniya da Croat don kafa wata kasa.

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya ayyana Srebrenica a matsayin wurin da "yake da tsaro" a lokacin bazara ta shekara ta 1993.

Amma sojojin Sabiya karkashin jagorancin Janar Ratko Mladic, wadanda daga baya aka same su da laifukan yaki da cin zarafin bil'adama da kisan kare-dangi, sun mamaye yankin na MDD.

Dakarun Holland sun gaza yin aikinsu yadda ya kamata sakamokon mamaye yankin da dakarun Sabiya suka yi, inda a ranar 11 ga watan Yuli suka kashe maza da yara maza 2,000.

Kimanin 'yan Bosniya 15,000 ne suka gudu zuwa tsaunukan da ke kewaye da su, amma sojojin Sabiyawa suka yi farautarsu suka kashe mutane 6,000 a cikin dazuzzuka.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Sojojin Turkiyya 20 sun yi shahada a hatsarin jirgin soji na dakon kaya a Georgia: Ma’aikatar Tsaro
Jirgin dakon kaya na sojin Turkiyya ya yi hatsari a iyakar Georgia-Azerbaijan dauke da jami'ai 20
Turkiyya na jimamin tunawa da rasuwar Ataturk shekara 87 da suka wuce
Nasarar da aka samu a yankin Karabakh na Azerbaijan babbar nasara ce ga yankin Caucasus: Erdogan
Turkiyya ta yi umarnin kama Firaministan Isra'ila Netanyahu da wasu mutane kan kisan kiyashi a Gaza
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan